Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Da Isra’ila Kanta
Published: 28th, June 2025 GMT
Iran ta yi kira da a gudanar da bincike mai zaman kansa kuma a hukumance kan zaluncin ‘yan sahayoniyya da Amurka
Mataimakin babban jami’in kula da harkokin kasa da kasa na ma’aikatar shari’a kuma sakataren hukumar kare hakkin bil’adama ta Iran ya yi la’akari da matakin wuce gona da iri na baya-bayan nan da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka yi kan cibiyoyin makamashin nukiliya, da kafofin yada labarai, da cibiyoyin kiwon lafiya na Iran, da kuma wuraren zama, gidajen yari da birane da kauyuka, a matsayin misali karara na keta dokokin kasa da kasa da hakkokin bil’adama.
A cikin wata wasika da ya aike wa kwamishinan kare hakkin bil-Adama na Majalisar Dinkin Duniya Volker Türk Nasser Seraj mataimakin shugaban hukumar shari’a kan harkokin kasa da kasa kuma sakataren hukumar kare hakkin bil’adama ta kasar Iran ya bayyana cewa da gan-gan yahudawan sahayoniyya sun kai hari kan ginin gidan rediyo da talabijin na Iran da makamai masu linzami.
Ya yi nuni da cewa, wannan harin ya ruguza wasu cibiyoyin yada labaran kasar, tare da kawo cikas wajen yada labarai, sannan kuma abin takaici ma ya kai ga shahada da raunata ma’aikatan kafafen yada labarai wadanda su kadai ke da alhakin sanar da jama’a abubuwan da ke faruwa.
A daya bangaren Saraj ya ci gaba da cewa: Hare-haren da ‘yam sahayoniyya suka kai a kwanakin baya kan cibiyoyin kiwon lafiya, ginin kungiyar agaji ta Red Crescent, da motocin daukar marasa lafiya, da kuma yankunan da ke kusa da asibitoci, sun haddasa lalacewar ababen more rayuwa, wanda ya yi sanadin mutuwa da jikkatar fararen hula, tare da sanya tsoro da firgici a tsakanin jama’a.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron ‘Farkawar Musulmi’ A Nan Tahren Inda Ka Tattauna Batun Falasdinu
A jiya Asabar ce aka gudanar da taron farkawar musulmi wanda aka saba gudanarwa a ko wace shekara don tattauna al-amuran kawancen kasashe masu gwagwarmaya da kuma kasashen musulmi a yankin da kuma sauran kasashen duniya.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran, ya bayyana cewa taron wanda aka gudanar a dakin taron shahida Muhammad Addurrah a nan Tehran ya sami halattar baki daga cikin gida da kuma kasashen waje.
Bakin dai sun hada da Nasser Abu Sharid wikilin kungiyar Jihadul Islami a nan Tehran,
Mohammad Hassan Akhtari, shugaban kwamitin kwamitin goyon bayan juyin juya hali a kasar Falasdinu. Mehdi Shoushtari daga ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran. Da kuma wasu daga baki daga ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran.
Nasser Abu Sharif wakilin Jihadul Islami, a Tehran ya bayyana cewa, shugaban kasar Amurka Donal Trump ya tsamar da HKI daga wargajewa tare da yarjeniyar da ya gabata. Yace falasdinawa sun amince da yarjeniyar, amma gwagwarmaya bata kare ba matukar HKI tana nan. Kuma tana ci gaba da kasha Falasdinawa a Gaza da yamma da kogin Jordan.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh October 12, 2025 China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100% October 12, 2025 An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter A Kasar Habasha October 12, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta October 12, 2025 An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Hamas Ta yi Watsi Da Yunkurin Balair Na Yiyuwar Shiga Gwamnatin Gaza. October 11, 2025 Cuba Ta Bayyana Bada Kyautar Noble Ga ‘Yar Kasar Veunzuelas machado A Matsayin Abin Kunya. October 11, 2025 Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta October 11, 2025 Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar. October 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci