Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Da Isra’ila Kanta
Published: 28th, June 2025 GMT
Iran ta yi kira da a gudanar da bincike mai zaman kansa kuma a hukumance kan zaluncin ‘yan sahayoniyya da Amurka
Mataimakin babban jami’in kula da harkokin kasa da kasa na ma’aikatar shari’a kuma sakataren hukumar kare hakkin bil’adama ta Iran ya yi la’akari da matakin wuce gona da iri na baya-bayan nan da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka yi kan cibiyoyin makamashin nukiliya, da kafofin yada labarai, da cibiyoyin kiwon lafiya na Iran, da kuma wuraren zama, gidajen yari da birane da kauyuka, a matsayin misali karara na keta dokokin kasa da kasa da hakkokin bil’adama.
A cikin wata wasika da ya aike wa kwamishinan kare hakkin bil-Adama na Majalisar Dinkin Duniya Volker Türk Nasser Seraj mataimakin shugaban hukumar shari’a kan harkokin kasa da kasa kuma sakataren hukumar kare hakkin bil’adama ta kasar Iran ya bayyana cewa da gan-gan yahudawan sahayoniyya sun kai hari kan ginin gidan rediyo da talabijin na Iran da makamai masu linzami.
Ya yi nuni da cewa, wannan harin ya ruguza wasu cibiyoyin yada labaran kasar, tare da kawo cikas wajen yada labarai, sannan kuma abin takaici ma ya kai ga shahada da raunata ma’aikatan kafafen yada labarai wadanda su kadai ke da alhakin sanar da jama’a abubuwan da ke faruwa.
A daya bangaren Saraj ya ci gaba da cewa: Hare-haren da ‘yam sahayoniyya suka kai a kwanakin baya kan cibiyoyin kiwon lafiya, ginin kungiyar agaji ta Red Crescent, da motocin daukar marasa lafiya, da kuma yankunan da ke kusa da asibitoci, sun haddasa lalacewar ababen more rayuwa, wanda ya yi sanadin mutuwa da jikkatar fararen hula, tare da sanya tsoro da firgici a tsakanin jama’a.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hizbullah: Isra’ila na kuskure idan ta na tunanin kashe-kashen kwamandodinmu zai kawo karshen kungiyar
Kungiyar Hizbollah ta kasar Lebanon ta bayyana cewa Isra’ila na yin kuskure idan ta na tunanin kashe-kashe da kisan gillar da ake wa mambobi da kwamandojinta zai kawo karshen kungiyar.
Wannan na zuwa ne bayan kisan gillar da Isra’ila ta yi wa babban kwamandan sojin kungiyar da wasu makusantansa a ranar Lahadi, a wani hari da ta kai a kudancin babban birnin Lebanon.
Haitham Ali Al-tabataba’i da aka fi sani da Abu Ali, ya yi shahada ne tare da wasu dakarun hizbullah guda 4 a wani mummunan hari da Isara’ila ta kai a heret hareik dake kudancin birnin beirut.
Tabataba’I yana daya daga cikin jajircaccen dakarun kungiyar hizbullah , kuma ya taka rawa sosai wajen tsarin tsaron kungiyar tun shekarun farko da aka kafata.
Kisan nasan ya kara nuna irin yadda isra’ila ke keta yarjejeniyar dakatar da tsagaita bude wuta da aka cimma, kuma kisan nasa zai kara karfafa jajircewa a turbar gwagwarmaya a yankunan labanon da falasdinu.
Da yake bayyana hakan Shugaban Majalisar Zartarwa ta Hizbullah, Sheikh Ali Damoush ya ce duk lissafin Isra’ila game da kungiyar ya cutura, saboda ta yi imani da cewa kisan gillar manyan mutane da kwamandojin soja na kungiyar zai iya kai ta ga nasara in ji, a ranar Litinin.
“Irin wadannan kisan gillar suna karfafa kudurin kungiyar na fuskantar mamayar Isra’ila,” in ji shi yayin da yake jawabi a jana’izar Shahid Haytham Ali Tabatabai.
Ya yi wa Tabatabai godiya, yana mai jaddada cewa ya taka rawa a lokacin yakin farko na Hezbollah.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tashar Talabijin ta Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru Mafaka Ta Wucin Gagi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi November 25, 2025 Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin November 25, 2025 An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci