More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tun kafin sanar da sabuwar ƙawance da suka haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da Peter Obi da Nasir El’rufai da wasu manyan ‘yan siyasa ne aka fara zargin yi wa wannan haɗaka zagon ƙasa da kawo cikas ga tafiyar.

Ɗaya daga cikin irin waɗannan zagon ƙasa da ake zargin wasu da yi wa wannan sabuwar haɗaka, ita ce na sanar da su rashin samun ɗakin taron da suka shirya gudanar da taron lokaci ƙalilan gabanin taron.

NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan noyayyun ƙalubalen da sabon haɗakar jam’iyyar ADC za ta iya fuskanta gabanin 2027.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Ce: Ba Za Ta Koma Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Sai A Kan Wasu Sharudda

Dakatar da ayyukan wuce gona da iri kan Iran wani sharadi ne na ci gaba da tattaunawar makamashin nukiliya

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin siyasa Majid Takht-e Ravanchi ya bayyana cewa: Sharadin ci gaba da gudanar da zaman shawarwarin makamashin nukiliyar Iran shi ne dakatar da duk wani matakin wuce gona da iri kan Iran, kuma har yanzu Amurka ba ta dauki wani mataki ba kan wannan batu.

A wata hira da tashar BBC game da batun tattaunawar makamashin nukiliyar Iran da Amurka: Takht-e Ravanchi ya ce: “Sun ji daga Amurka cewa a shirye take ta ci gaba da tattaunawar, amma har yanzu ba a tsayar da ranar ba, kuma Iran ba ta amince da tsarin shawarwarin ba.”

Ya kara da cewa: “A halin yanzu Iran tana neman amsoshi dangane da ko za ta sake fuskantar sabbin matakan wuce gona da iri yayin da aka fara tattaunawar.” Har yanzu dai Amurka ba ta bayyana matsaya ba kan wannan batu.

Da aka tambaye shi game da yiwuwar cimma yarjejeniya tsakanin bangarorin biyu, ciki har da dage takunkumin da aka kakabawa Iran, a madadin Iran ta dakatar da inganta sinadarin Uranium, Takht-e Ravanchi ya ce: “Me zai sa su amince da wannan shawara? Inganta sinadarin Uranium zuwa kashi 60 cikin 100 ana amfani da shi ne domin zaman lafiya. Tabbas za a iya tattaunawa kan matakinsa, amma maganarsu ta cewa dole ne Iran ta daina inganta Uranium gaba daya, in ba haka ba za ta fuskanci hari, wannan maganar hankali me? Wannan dokar daji ce.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC
  • Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
  • Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
  • Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu
  • DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa
  • Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata 2 bayan ambaliya
  • Iran Ta Ce: Ba Za Ta Koma Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Sai A Kan Wasu Sharudda