More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tun kafin sanar da sabuwar ƙawance da suka haɗa da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da Peter Obi da Nasir El’rufai da wasu manyan ‘yan siyasa ne aka fara zargin yi wa wannan haɗaka zagon ƙasa da kawo cikas ga tafiyar.

Ɗaya daga cikin irin waɗannan zagon ƙasa da ake zargin wasu da yi wa wannan sabuwar haɗaka, ita ce na sanar da su rashin samun ɗakin taron da suka shirya gudanar da taron lokaci ƙalilan gabanin taron.

NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan noyayyun ƙalubalen da sabon haɗakar jam’iyyar ADC za ta iya fuskanta gabanin 2027.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons

Shugaban hukumar kula da wasanni ta ƙasa (NSC), Bukola Olopade, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa Super Falcons ba su samu kuɗin alawus ɗin da aka yi musu alƙawari ba, yana mai cewa an riga an biya duk ƴan wasan, sai kaɗan daga cikinsu da ke da matsalar asusun banki. Ya ce ya tabbatar da hakan ne daga shugabar ƙungiyar, Rasheedat Ajibade, da kuma hukumar kwallon ƙafa ta ƙasa (NFF).

Olopade ya ce ba daidai ne a yi iƙirarin cewa ba a biya kuɗin ba, inda ya ƙara da cewa bai kamata a jefa Ajibade cikin matsalar musanta kalaman da ba ta faɗa ba. Ya bayyana cewa waɗanda ke da matsalar asusun banki su kaɗai ba su samu ba, amma sauran duk sun karɓi hakkokinsu.

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Game da kyautar $100,000 da gidajen masu ɗakuna uku da Shugaba Bola Tinubu ya yi wa kowacce ƴar wasa bayan lashe kofin WAFCON na 2025, Olopade ya ce gwamnati na kan shirin cika alƙawarin nan da ba da komawa ba. Ya bayyana cewa ana ci gaba da tattaunawa da ma’aikatar gidaje da shirin Renewed Hope Homes domin ganin an kammala aikin cikin lokaci.

Ya jaddada cewa gwamnatin Tinubu tana da tarihin cika alƙawari ga ƴan wasa, inda ya ce ba sa sakaci da batun lada ko shirin tura su gasar ƙasa da ƙasa. A ranar 28 ga Yuli, 2025, Shugaba Tinubu ya karɓi tawagar Super Falcons a Fadar Aso Rock, inda ya sanar da kyautar kuɗi, da gida, da lambar yabo ga kowacce ƴar wasa, lamarin da daga baya ya jawo ce-ce-ku-ce bayan rahoton da aka danganta wa Ajibade.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HOTUNA: Yadda zaɓen cike gurbi ke gudana a sassan Najeriya
  • Mali: An kama wasu Manyan Janar-Janar dan kasar Faransa bisa zargin yunkurin juyin mulki
  • Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe
  • Tinubu ya bar Abuja zuwa Japan da Brazil
  • An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons
  • Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
  • NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
  • Kotun kasar Kanada ta ayyana APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci
  • NAJERIYA A YAU: Halin ƙuncin da ’yan fansho ke ciki a Najeriya
  • An zabi sabuwar firaminista a Luthuania