HausaTv:
2025-08-17@16:27:38 GMT

 Arakci Ya Mayar Wa Da Jami’ar Harkokin Wajen ” EU” Martani

Published: 3rd, July 2025 GMT

Minstan harkokin wajen Iran Abbas Arakci ya mayar da martani da kakkausar murya akan furucin jami’ar diplomasiyya ta tarayyar turai Kaya Jallas na cewa Iran ta dakatar da shirinta na makamashin Nukiliya, yana mai cewa; Jallas ta jahilci abinda dokokin NPT su ka kunsa.

Abbas Arakci ya ce; Idan manufar ganawa da kwamitin hadin gwiwa akan yarjeniyar Nukilar iran shi ne kawo karshen Shirin makamashin Nukiliyar Iran, to kuwa Jallas ta jahilci abinda yake kunshe a cikin yarjejeniyar hana yaduwar makaman Nukiliya.

Ita dai babbar jami’ar harkokin wajen tarayyar turai Jallas ta rubuta sako a shafinta na X cewa; Ya zama wajibi a bude tattaunawa da sauri da Iran akan yadda za ta kawo karshen shirinta na makamashin Nukiliya, kuma ficewa daga yarjejeniyar NPT ba zai zama mai taimakawa ba wajen warware batun da yake da alaka da Shirin makamashin Nukiliyar Iran.

Arakci ya kuma ce ; Wannan yana nufin cewa; rawar da tarayyar turai da kuma Birtaniya za su taka a cikin duk wata tattaunawa a nan gaba, za ta zama maras ma’ana.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

Bugu da kari kuma, gudummawar da Nijeriya ke bayarwa ga kokarin wanzar da zaman lafiya a duniya ba za su misalta tu ba, wanda hakan ke jaddada aniyarta na inganta zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. Manufofinta na kasashen waje a al’adance suna nufin ingantawa da kuma kare muradun Nijeriya tare da tallafa wa hadin kan Afirka.

Gabatar da ajandar “4D”, a sakamakon haka, yana wakiltar sauyin da aka samu a lokacin da ya dace, wanda hakan zai bude damar karfafa hadin gwiwar da kasashen duniya, tabbatar da zaman lafiya na duniya, da kuma bunkasa matsayin Nijeriya a idon duniya. Sai dai, nasarar wadannan manufofin ya ta’allaka ne a kan aiwatarwar su mai inganci.

Ya kamata a lura da cewa Nijeriya ta tsunduma cikin harkokin diflomasiyya da dama a bara, ciki har da kulla wasu muhimman yarjejeniyoyi da Jamhuriyar kasar Sin. Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya ziyarci Abuja, domin jaddada alkawuran da aka dauka a yayin taron dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka (FOCAC) na shekarar 2024, inda aka rattaba hannu kan wasu muhimman yarjejeniyoyi guda 10. Hakazalika, firaministan Indiya Narendra Modi ya ziyarci Nijeriya, inda ya bayyana aniyar kasarsa na zuba hannun jari a wasu muhimman sassa kamar a bangaren noma, samar da abinci, sadarwa, fasaha da bayanai, da kuma tsaro.

Shugaba Tinubu ya kuma gudanar da rangadin diflomasiyya, inda ya halarci taron G20 a Brazil da kuma kai ziyara a Faransa da Afirka ta Kudu da dai sauransu. Wadannan alkawurra an yi su ne da nufin karfafa martabar Nijeriya a idon duniya da kuma samar da fa’idodi na gaske ga kasar.

Duk da yake wadannan tafiye-tafiye na diflomasiyya abin yabawa ne, amma kuma dole ne su kasance su samar wa da kasar jari mai ma’ana da fa’ida ga ‘yan Nijeriya.

Sai dai a halin yanzu, hakan ya yi nisa daga zahirin abin da yake faruwa. Dole ne gwamnatin Tinubu ta dauki matakai masu muhimmanci domin tabbatar da cewa manufofin kasashen waje na Nijeriya sun fifita muradun kasa tare da kare ‘yan kasarta a kasashen waje. Wannan shi ne ainihin manufar “4D”.

Za a iya danganta raguwar tasirin Nijeriya a fagen duniya da tabarbarewar tattalin arzikin da aka shafe tsawon shekaru ana yi, wanda ya tilastawa ‘yan kasar da dama neman ingantacciyar damammaki a kasashen waje, galibi a cikin yanayi mai wahala da wulakanci. Idan ana son a sauya wannan hali, dole ne gwamnatin Tinubu ta gaggauta farfado da tattalin arzikin kasar domin fitar da miliyoyin mutane daga kangin talauci.

Ana iya cimma wannan ta hanyar jawo hankalin masu zuba hannun jari daga kasashe irin su Indiya, Sin, Afirka ta Kudu, da Faransa, musamman a fannoni kamar hakar ma’adinai, aikin gona, da ICT, wadanda ke da fa’ida masu yawan gaske. Har ila yau, dole ne Nijeriya ta mayar da hankali wajen bunkasa harkokin kasuwanci na yanki, kamar samar da kasuwar samun kayayyakin amfanin gona da za su hada masu samarwa da masu shigo da kayayyaki, ta yadda za a rage dogaro da kuma fadada kasuwancin kayayyakin Nijeriya.

Domin manufofin Nijeriya na kasashen waje su yi tasiri, dole ne ta fara magance bukatun ‘yan kasarta. Gwamnatocin da suka gada sun yi ta fafutika wajen yin amfani da damar hadin gwiwar kasa da kasa domin samar da ayyukan yi, da jawo jari, da kawar da talauci. Alkaluman sun yi muni: a tsakanin 2023 zuwa 2024, kashi 63% na ‘yan Nijeriya – kimanin mutane miliyan 133.3 – suna rayuwa cikin kangin talauci, a cewar Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS). Rashin aikin yi na matasa ya kasance wani muhimmin batu, a yayin da hauhawar farashin kayayyaki ya kai kashi 34.6% a karshen shekarar 2024, inda hauhawar farashin kayayyakin abinci ma ya fi kamari.

Rahoton Tattalin Arziki na Afirka (ERA 2023) ya jaddada gaggawar magance kalubalen tattalin arzikin Nijeriya. Ya gano manyan gibi guda uku – kwarewa, abubuwan more rayuwa, da kuma ingancin cibiyoyin (gudanarwa) – wadanda dole ne a gyara su domin gina tubuli mai karfi domin ci gaba.

Mun yi imani wannan ita ce hanya madaidaiciya. Dole ne gwamnatin Tinubu ta fito da tsare-tsare masu kyau na ci gaban kasa, samar da shugabanci nagari, da aiwatar da gyare-gyaren tsari a dukkan bangarori masu muhimmanci.

A yayin da Nijeriya ke fuskantar tabarbarewar tattalin arziki da kuma yanayi na cire fata a tsakanin ‘yan kasar, dole ne gwamnatin Tinubu ta tashi tsaye tare da rungumar tsarin hulda da kasashen waje na Ambasada Yusuf Tuggar. Manufofin kasashen waje da zai jawo zuba hannun jari, samar da ayyukan yi, da magance tushen talauci, tabbas wadannan a karshe za su samar da nasara. Da duk wani abu da ka iya rage barazana ga barin Nijeriya ta makale a tsaka mai wuya a tsakanin yiwuwarsa da tabarbarewar ta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnonin Arewa sun yi ta’aziyyar rasuwar Sarkin Zuru
  • An kama manyan shugabannin ’yan ta’addan ƙungiyar Ansaru — Ribadu
  • Jami’in Harkokin Shari’ar Kasa Da Kasa Na Iran Ya Yi Tofin Allah Tsine Kan Furucin Jami’ar Shari’ar Kasa Da Kasa
  • Takht-Ravanchi: Iran a shirye take ta ci gaba da tattaunawa kan hakkinta na nukiliya
  • Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
  • Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
  • Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu
  • Babban Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Iran Ya Ce; Iran Zata Mayar Da Martani Mai Tsanani Kan Duk Wanda Ya Kai Mata Hari
  • Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata
  • Iran: Suna Bukatar Kawo Karshen Makaman Nukiliya Da Kuma Furuci Maras Daɗin Ji