Aminiya:
2025-10-13@15:49:53 GMT

’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara

Published: 3rd, July 2025 GMT

Aƙalla jami’an tsaro shida ne suka rasu bayan wata arangama da suka yi da ’yan bindiga a yankin Gada Woro a kan hanyar Patigi da ke Ƙaramar Hukumar Edu a Jihar Kwara.

Waɗanda suka rasu sun haɗa da ’yan banga guda biyar da ɗan sanda ɗaya.

‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’ Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato

Wasu sojoji biyu, ’yan sanda biyu sun samu raunin harbin bindiga a fafatawar da ta faru a ranar Litinin.

Waɗanda suka rasu sun haɗa da Mohammed Nma Dsuru daga Kokodo, Yanda daga Lafiagi, da Ndagi Saraka daga Edogi.

Rahotanni sun ce ’yan bindigar da yawansu ya kai ɗaruruwa sun kai wa tawagar jami’an tsaro farmaki a cikin daji, inda aka yi ta musayar wuta.

Wasu daga cikin waɗanda suka jikkata an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilorin (UITH) domin samun kulawa.

Wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta ya nuna yadda aka fafata a dajin.

Wasu mazauna yankin sun ce lamarin ya fara ne a ranar Asabar, lokacin da aka sace wani fitaccen mai sayar da magungunan gona wanda ya dawo daga aikin Hajji.

’Yan bindigar sun shigo da babura, suka shiga gidansa da ke unguwar Taiwo da misalin ƙarfe 1 na dare sannan suka tafi da shi.

A ranar Lahadi, sun sake kai wani hari inda suka sace ɗan kasuwa mai sana’ar POS, Alhaji Yaman da wani mutum mai suna Usman.

’Yan banga sun samu nasarar ceto mutum ɗaya daga cikinsu.

Wasu daga cikin al’ummar yankin na zargin cewa wasu mazauna garin na taimaka wa ’yan bindigar a ɓoye, duba da cewa yawancin waɗanda aka sace matasa ne kuma fitattun ’yan kasuwa a yankin.

An yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin ’yan sandan jihar, Adetoun Ejire Adeyemi, amma ba ta ɗauki waya ko amsa saƙon da aka aike mata ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Arangama hari Jami an Tsaro Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wasu ma’aurata da wasu mutane biyar bisa zarginsu da gudanar da ɗaurin aure ba tare da izinin iyayensu ba ko kuma bin tsarin addinin Musulunci a unguwar Nasarawa da ke cikin birnin Kano. Wadanda ake zargin sun hada da ango mai suna Aminu mai shekaru 23 da amaryarsa Sadiya mai shekaru 22. Sauran wadanda aka kama su ne Umar mai shekaru 24 wanda ya kasance wakilin ango; Abubakar, mai shekaru 23, wanda ya kasance waliyyin amarya; Usaina, mai shekaru 21; da kuma wasu ‘yan mata guda biyu wadanda suka kasance shaidu a yayin ɗaurin auren. Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya Rahotanni sun bayyana cewa, an ɗaura auren ne akan sadaki Naira 10,000, ba tare da amincewar iyayen ma’auratan ba. Da yake tabbatar da faruwar lamarin, mataimakin babban kwamandan hukumar ta Hisbah, Dr. Mujaheeddeen Aminuddeen, ya ce an kama wadanda ake zargin ne biyo bayan korafe-korafen da ‘yan unguwar suka kai wa hukumar. Ya bayyana cewa, matakin da wadanda ake zargin suka ɗauka ya saɓawa koyarwar addinin Musulunci da kuma dokokin aure na jihar, yana mai jaddada cewa, hukumar ta Hisbah ba za ta amince da duk wani abu da ya saɓawa tsarin addini da na shari’a a jihar Kano ba. Dr. Aminudeen ya kara da cewa, a halin yanzu wadanda aka kama suna hannun Hisbah domin ci gaba da bincike. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Ra'ayi Riga Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang October 13, 2025 Labarai Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista October 13, 2025 Manyan Labarai Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya October 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
  • ’Yan bindiga sun kashe sojoji 3 a Kebbi 
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara