Aminiya:
2025-11-27@22:34:14 GMT

’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara

Published: 3rd, July 2025 GMT

Aƙalla jami’an tsaro shida ne suka rasu bayan wata arangama da suka yi da ’yan bindiga a yankin Gada Woro a kan hanyar Patigi da ke Ƙaramar Hukumar Edu a Jihar Kwara.

Waɗanda suka rasu sun haɗa da ’yan banga guda biyar da ɗan sanda ɗaya.

‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’ Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato

Wasu sojoji biyu, ’yan sanda biyu sun samu raunin harbin bindiga a fafatawar da ta faru a ranar Litinin.

Waɗanda suka rasu sun haɗa da Mohammed Nma Dsuru daga Kokodo, Yanda daga Lafiagi, da Ndagi Saraka daga Edogi.

Rahotanni sun ce ’yan bindigar da yawansu ya kai ɗaruruwa sun kai wa tawagar jami’an tsaro farmaki a cikin daji, inda aka yi ta musayar wuta.

Wasu daga cikin waɗanda suka jikkata an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilorin (UITH) domin samun kulawa.

Wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta ya nuna yadda aka fafata a dajin.

Wasu mazauna yankin sun ce lamarin ya fara ne a ranar Asabar, lokacin da aka sace wani fitaccen mai sayar da magungunan gona wanda ya dawo daga aikin Hajji.

’Yan bindigar sun shigo da babura, suka shiga gidansa da ke unguwar Taiwo da misalin ƙarfe 1 na dare sannan suka tafi da shi.

A ranar Lahadi, sun sake kai wani hari inda suka sace ɗan kasuwa mai sana’ar POS, Alhaji Yaman da wani mutum mai suna Usman.

’Yan banga sun samu nasarar ceto mutum ɗaya daga cikinsu.

Wasu daga cikin al’ummar yankin na zargin cewa wasu mazauna garin na taimaka wa ’yan bindigar a ɓoye, duba da cewa yawancin waɗanda aka sace matasa ne kuma fitattun ’yan kasuwa a yankin.

An yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin ’yan sandan jihar, Adetoun Ejire Adeyemi, amma ba ta ɗauki waya ko amsa saƙon da aka aike mata ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Arangama hari Jami an Tsaro Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina

Hukumar kula da makarantun firamare da sakandare ta Jihar Katsina ta sanar da sake buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarabawar zangon farko na shekarar karatu.

A wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Sani Danjuma Suleman, ya fitar a madadin Shugaban hukumar, ta ce makarantun firamare, sakandiren je-ka-ka-dawo da kuma makarantu masu zaman kansu za su buɗe daga yau Talata domin ci gaba da jarabawar zangon farko.

Sanarwar ta ƙara da cewa, sauran makarantun kwana za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai lokacin da hali ya ba da dama.

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Gwamnatin Katsina ta rufe makarantun bayan ƙaruwar hare-haren sace ɗalibai da masu garkuwa da mutane suka sake farfaɗowa da su a wasu yankuna.

Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne da nufin daƙile matsalar tsaro da kuma sa ido a kan al’amura.

A ƙarshe, hukumar ta roƙi haɗin kan iyaye da masu kula da ɗalibai domin su ci gaba da ba wa shirin goyon baya tare da ƙarfafa ɗaliban su dage da karatu wajen rubuta jarabawar da suke yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • ’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara