Aminiya:
2025-08-17@16:29:38 GMT

’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara

Published: 3rd, July 2025 GMT

Aƙalla jami’an tsaro shida ne suka rasu bayan wata arangama da suka yi da ’yan bindiga a yankin Gada Woro a kan hanyar Patigi da ke Ƙaramar Hukumar Edu a Jihar Kwara.

Waɗanda suka rasu sun haɗa da ’yan banga guda biyar da ɗan sanda ɗaya.

‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’ Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato

Wasu sojoji biyu, ’yan sanda biyu sun samu raunin harbin bindiga a fafatawar da ta faru a ranar Litinin.

Waɗanda suka rasu sun haɗa da Mohammed Nma Dsuru daga Kokodo, Yanda daga Lafiagi, da Ndagi Saraka daga Edogi.

Rahotanni sun ce ’yan bindigar da yawansu ya kai ɗaruruwa sun kai wa tawagar jami’an tsaro farmaki a cikin daji, inda aka yi ta musayar wuta.

Wasu daga cikin waɗanda suka jikkata an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilorin (UITH) domin samun kulawa.

Wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta ya nuna yadda aka fafata a dajin.

Wasu mazauna yankin sun ce lamarin ya fara ne a ranar Asabar, lokacin da aka sace wani fitaccen mai sayar da magungunan gona wanda ya dawo daga aikin Hajji.

’Yan bindigar sun shigo da babura, suka shiga gidansa da ke unguwar Taiwo da misalin ƙarfe 1 na dare sannan suka tafi da shi.

A ranar Lahadi, sun sake kai wani hari inda suka sace ɗan kasuwa mai sana’ar POS, Alhaji Yaman da wani mutum mai suna Usman.

’Yan banga sun samu nasarar ceto mutum ɗaya daga cikinsu.

Wasu daga cikin al’ummar yankin na zargin cewa wasu mazauna garin na taimaka wa ’yan bindigar a ɓoye, duba da cewa yawancin waɗanda aka sace matasa ne kuma fitattun ’yan kasuwa a yankin.

An yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin ’yan sandan jihar, Adetoun Ejire Adeyemi, amma ba ta ɗauki waya ko amsa saƙon da aka aike mata ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Arangama hari Jami an Tsaro Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Wani mutum yanke makazutarsa a Borno

An ceto wani mutum mai shekara 50 ya yi yunƙurin kashe kansa a garin Bama na Jihar Borno.

Lamarin wanda ya afku a yammacin ranar Juma’a a unguwar Hausari, inda al’ummar yankin ne suka kai masa ɗauki.

Shaidu sun ce mutumin ya daɓa wa kansa wuƙa har sau uku a ciki, kafin ya yanke mazakutarsa da wuƙar.

An ce ya aikata hakan ne saboda tsohuwar matarsa, daga garin Konduga, wadda ya yi wa saki uku, ta ƙi komawa gidansa.

Ta’aziyyar Sarkin Zuru: Muhammadu Sani Sami (1943-2025) Tun watan Ramadan muke cikin duhu — Al’ummar Jauro Jatau

’Yan sanda sun jagoranci tawagar ’yan sintiri zuwa wurin, inda suka gano tare da ƙwace wuƙar, sa’annan suka kwashi magidancin zuwa Babban Asibitin Bama, inda yake karɓar magani.

Majiyoyi sun ce an miƙa lamarin zuwa sashin binciken manyan laifuka (CID) da ke Maiduguri, domin ci gaba da bincike

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani mutum yanke makazutarsa a Borno
  • Yadda noma ya kankama bayan sulhu da ’yan bindigar Katsina
  • Mali: An kama wasu Manyan Janar-Janar dan kasar Faransa bisa zargin yunkurin juyin mulki
  • Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
  • Mutum 12 sun rasu, 5 sun jikkata a hatsarin mota a Kano
  • Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe
  • An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi
  • Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
  • Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
  • NAJERIYA A YAU: Halin ƙuncin da ’yan fansho ke ciki a Najeriya