Kotu a kasar Iraki ta yanke hukuncin kisa kan wadanda suka kashe Ayatullah Baqir Sadr da ‘yar uwarsa Alawiyya Bint al-Huda

Hukumar tsaron kasar Iraki ta sanar a ranar litinin cewa: Kotun hukunta manyan laifuka ta kasar ta yanke hukuncin kisa kan wadanda suka aiwatar da zaluncin kisa kan Ayatullahi Muhammad Baqir al-Sadr da ‘yar uwarsa Alawiyya Bint al-Huda.

Ofishin yada labarai na hukumar tsaron kasar Iraki ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Kotun hukunta manyan laifuka ta kasar ta yanke hukuncin kisa kan masu laifin Sa’adoun Sabri da Haitham Abdul Aziz, bayan da aka tabbatar da cewa suna da hannu wajen aiwatar da hukuncin kisa kan Shahadar Sayyid Muhammad Baqir al-Sadr da ‘yar uwarsa, Alawiyya Bint al-Huda a shekara ta 1980, tare da aiwatar da hukuncin kisa kan ‘yan kasar da suka hada da talakawa da masu arziki da kuma mambobin jam’iyyar Da’awa a lokacin rusasshiyar gwamnatin Saddam Husain.”

Hukumar ta kara da cewa: “Hukuncin ya zo ne a cikin tsarin kokarin tabbatar da adalci, kuma shi ne kololuwar ayyukan hukumar tsaron kasar, inda ta samu nasarar cafke wadanda ake tuhuma tare da gudanar da binciken da ya dace a karkashin kulawar kwararrun bangaren shari’a.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Iraki

এছাড়াও পড়ুন:

Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  

Kotun daukaka kara ta Marseille ta tabbatar da soke dokar da ta bayar da umarnin rufe makarantar sakadare ta Musulinci da ke birnin Nice.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, lauyan makarantar, Sefen Guez Guez, ya yaba da nasarar ta uku a jere” tare da bayyana fatan cewa “za a daina tsananta wa wannan makaranta gaba daya.

Takadammar data shafi makarantar ta hana da Rashin haske kan kudadenta, wanda hukumomjin yankin ke zargin makarantar da ta ina take samun kudadenta kamar yadda doka ta tanada.

” An bude makarantar ne a cikin shekarar 2016 a gundumar Ariane, kuma makarantar mai zaman kanta a halin yanzu tana da dalibai 130.

Rahotanni sun ce makarantar, wadda wata kungiya ce mai alaka da kungiyar Musulman Alpes-Maritimes (UMAM) ke tafiyar da ita, ta yi ikirarin cewa tana neman ta bi duk ka’idojin da aka shimfida.

Ana kallon wannan hukuncin da kotun daukaka kara ta dauka a matsayin wata alamar kwantar da hankali a muhawarar da ake yi kan rawar da makarantun da ba su da alaka da addini suke takawa a Faransa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine October 12, 2025 Arachi: HKI Ba Abar Amincewa Ba Ce, Falasdinawa Su Yi Hattara October 12, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon October 12, 2025 An Gudanar Da Taron ‘Farkawar Musulmi’ A Nan Tahren Inda Aka Tattauna Batun Falasdinu October 12, 2025 Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh October 12, 2025 China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100% October 12, 2025 An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter  A Kasar Habasha October 12, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta October 12, 2025 An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Afirka Ta Kudu Ta Ce Babu Wata Makarkashiya A Mutuwar Jakadanta A Kasar Faransa October 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Iran Ta Ki Zuwa Masar Saboda Bata Son Haduwa Da Azzaluman Da Suka Kashe Falasdinwa A Gaza
  • Falasdinawa Sun Gano Gawakin Wadanda HKI Ta Kashe A gaza  Fiye Da 320 Cikin Kwanaki Biyu Kacal
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta