Kotu A Kasar Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Ayatullahi Baqir Sadr
Published: 1st, July 2025 GMT
Kotu a kasar Iraki ta yanke hukuncin kisa kan wadanda suka kashe Ayatullah Baqir Sadr da ‘yar uwarsa Alawiyya Bint al-Huda
Hukumar tsaron kasar Iraki ta sanar a ranar litinin cewa: Kotun hukunta manyan laifuka ta kasar ta yanke hukuncin kisa kan wadanda suka aiwatar da zaluncin kisa kan Ayatullahi Muhammad Baqir al-Sadr da ‘yar uwarsa Alawiyya Bint al-Huda.
Ofishin yada labarai na hukumar tsaron kasar Iraki ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Kotun hukunta manyan laifuka ta kasar ta yanke hukuncin kisa kan masu laifin Sa’adoun Sabri da Haitham Abdul Aziz, bayan da aka tabbatar da cewa suna da hannu wajen aiwatar da hukuncin kisa kan Shahadar Sayyid Muhammad Baqir al-Sadr da ‘yar uwarsa, Alawiyya Bint al-Huda a shekara ta 1980, tare da aiwatar da hukuncin kisa kan ‘yan kasar da suka hada da talakawa da masu arziki da kuma mambobin jam’iyyar Da’awa a lokacin rusasshiyar gwamnatin Saddam Husain.”
Hukumar ta kara da cewa: “Hukuncin ya zo ne a cikin tsarin kokarin tabbatar da adalci, kuma shi ne kololuwar ayyukan hukumar tsaron kasar, inda ta samu nasarar cafke wadanda ake tuhuma tare da gudanar da binciken da ya dace a karkashin kulawar kwararrun bangaren shari’a.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Iraki
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe wani tsohon malami kuma manomi, Andrew Imuekheme, a Jihar Edo.
Lamarin ya faru ne a ranar Talata a garin Ikabigbo, da ke Masarautar Uzairue, a Ƙaramar Hukumar Etsako ta Yamma.
Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin NajeriyaRahotanni sun ce Malam Andrew na kan hanyarsa daga gona lokacin da maharan suka tare shi, tare da ɗauke shi zuwa daji.
Wata mata da ta tsere daga hannun maharan ta koma cikin gari tare da sanar wa mafarauta, waɗanda suka fara bincike nan take.
Tuni jami’an tsaro suka umarci manoma da ke da gonaki a kusa da yankin da su koma gidajensu saboda tsaro.
Daga baya, ’yan sa-kai sun gano babur da takalman mamacin.
Bayan zurfafa bincike cikin dare suka gano gawarsa.
Sarkin garin, Cif Braimah Alegeh, ya yi Allah-wadai da kisan tare da bayyana mutanensa a matsayin masu zaman lafiya.
Ya roƙi gwamnati da jami’an tsaro su kawo musu ɗauki.
Wannan shi ne karo na uku da irin wannan kisan ke faruwa a garin.
Shekaru biyu da suka gabata, an kashe wani malamin Katolika da shugaban mafarauta.
Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Moses Yamu, ya ce zai fitar da sanarwa daga baya.