HausaTv:
2025-08-15@21:38:09 GMT

An Kashe ‘Yan Kungiyar Shabab 19  A Kasar Somaliya

Published: 1st, July 2025 GMT

Sojojin kasar Somaliya sun sanar da kai wani farmaki a kudancin kasar da ya yi sanadiyyar kashe 19 daga cikin ‘yan kungiyar ‘al-shabab’.

 Sanarwar wacce tashar talbijin din ‘almayadin’ ta nakalto ta ce, sojojin na Somaliya sun kai harin ne a jiya Litinin da dare a yankin Jubayi, wanda kuma bayan kashe ‘yan kungiyar an kuma jikkata wasu da dama.

Ma’aikatar tsaron kasar Somaliya ta kuma ce; sojojin kasar sun yi nasarar kama makamai masu yawa a tare da kungiyar ta ‘al-shabab’.

 A cikin watan Disamba na shekarar da ta shude ma dai sojojin na Somaliya su ka yi nasarar kashe ‘yan kungiyar su 130 a jahohin Gulmadag, da Jubaland.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

Hukumar kula da kumbuna ta kasar Sin ta ce nan ba da jimawa ba, ‘yan sama jannatin kumbon Shenzhou-20 dake cibiyar binciken sararin samaniya ta kasar, za su gudanar da zagaye na 3 na ayyuka a wajen cibiyar.

‘Yan sama jannatin 3 da suka hada da Chen Dong da Chen Zhongrui da Wang Jie, sun gudanar da irin wannan aiki har sau biyu, a watannin Mayu da Yuni.

Baya ga haka, sun kammala ayyukan nazarin muhalli da kula da tantance da kayayyakin aiki a cikin cibiyar da jigilar kayayyaki. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Kansu Bayan Yakin Gaza
  • Kungiyar Ansarullahi Ta Kasar Yemen Ya Ce; Yahudawan Sahayoniyya Suna Yakar Al’ummar Falasdinu Duka Ne
  • Kungiyar Ba Da Agaji Ta Sanar Da Yadda Cutar Kwalara Take Lashe Rayukan Mutane A Kasar Sudan
  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin
  • NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya
  • Gwamna Namadi Ya Yaba Wa Kungiyar NBA Bisa Inganta Manufofi Da Ka’idojin Aikin Lauya
  • Kano Na Karbar Bakuncin Babban Taron Kungiyar NUJ Na Kasa
  • Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida