Yunwa ta kashe ƙananan yara 66 a Gaza
Published: 28th, June 2025 GMT
Hukumomi sun tabbatar da mutuwar ƙananan yara 66 a sakamakon yunwa a yankin Gaza.
Yaran sun mutu a yayin da sojojin Isra’ila ke ci gaba da hana shigar da madarar yara da sauran kayan abinci da sauran kayan jinƙai da ake buƙata domin ceto rayuka zuwa Gaza.
Mutuwar yaran ta zo ne a daidai lokacin da hukumomin Gaza suka sanar cewa sojojin Isra’ila sun kashe wasu Palasdinawa 34.
Jami’an lafiya a Asibitin Al-Shifa da ke Gaza sun bayyana cewa an kawo gawarwakin wasu mutum 12 da sojojin Isra’ila suka kashe a filin wasa da Palasdinawa ke zaman mafaka, da wasu takwas da aka kashe a wani gida.
‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’ Yadda aka yi jana’izar kwamandojin Iran da Isra’ila ta kasheOfishin yaɗa labarai na hukumomin Gaza ya bayyana cewa ana matuƙar buƙatar kayan abincin domin ceto rayuwar musamman ƙananan yara da gajiyayyu da marasa lafiya.
Sanarwar Hukumar ta ce, “laifin yaƙi ne da tauye haƙƙin ɗan Adam ne abin da Isra’ila ke yi na amfani da salon hana faren hula samun abinci a matsayin makami.
“Wannan ya saɓa da yarjejeniyar Geneva da kuma dokokin ayyukan jinƙai na duniya.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
Kwamishiniyar Ilimi ta Jihar Gombe, Dokta Aishatu Umar Maigari, ta ce talauci da nuna bambanci na daga cikin manyan dalilan da ke hana yara mata damar samun ilimi a jihar.
Ta bayyana hakan ne a wajen bikin Ranar Yara Mata ’Yan Makaranta ta Duniya ta shekarar 2025, wanda Shirin AGILE tare da Access Initiative Africa da Nudge Initiative suka shirya a Gombe.
Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a BornoA wajen bikin, Uwargidan Gwamnan Jihar Gombe, Asma’u Inuwa Yahaya, ta yaba da yadda gwamnatin jihar ke ƙoƙarin tabbatar da cewa ba a bar wata yarinya a baya wajen samun ilimi.
Ta ce Gwamnan jihar, ya bai wa ilimin yara mata muhimmanci, wanda hakan ya sa ake samu ƙaruwa yara mata da ke zuwa makaranta.
Kwamishiniyar, ta ƙara da cewa ma’aikatar ilimi tana aiki wajen samar da sabbin manufofi da tsare-tsare da za su taimaka wajen rage waɗannan matsaloli da tabbatar da damar ilimi ga kowa cikin adalci.
A nata jawabin, Kodinetan Shirin AGILE, Dokta Amina Haruna Abdul, ta ce bikin na bana an shirya shi ne don ƙarfafa gwiwar yara mata wajen ci gaba da neman ilimi duk da ƙalubalen da suke fuskanta.
Ta gode wa Uwargidan Gwamnan da ma’aikatar ilimi bisa goyon bayansu.
Haka kuma, Akawun Majalisar Dokokin Jihar Gombe, Barista Rukayyatu Jalo, ta shawarci yara mata da su dage wajen yin karatu, inda ta bayyana cewa ilimi ne hanyar da za ta gina rayuwarsa.
Wasu daga cikin ɗaliban da suka halarci bikin, sun bayyana farin ciki da godiya kan shirya taron saboda yadda ya ƙara musu ƙwarin gwiwa.
Ɗalibai da dama sun gudanar da muhawara da wasan kwaikwayo a wajen taron.