Yunwa ta kashe ƙananan yara 66 a Gaza
Published: 28th, June 2025 GMT
Hukumomi sun tabbatar da mutuwar ƙananan yara 66 a sakamakon yunwa a yankin Gaza.
Yaran sun mutu a yayin da sojojin Isra’ila ke ci gaba da hana shigar da madarar yara da sauran kayan abinci da sauran kayan jinƙai da ake buƙata domin ceto rayuka zuwa Gaza.
Mutuwar yaran ta zo ne a daidai lokacin da hukumomin Gaza suka sanar cewa sojojin Isra’ila sun kashe wasu Palasdinawa 34.
Jami’an lafiya a Asibitin Al-Shifa da ke Gaza sun bayyana cewa an kawo gawarwakin wasu mutum 12 da sojojin Isra’ila suka kashe a filin wasa da Palasdinawa ke zaman mafaka, da wasu takwas da aka kashe a wani gida.
‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’ Yadda aka yi jana’izar kwamandojin Iran da Isra’ila ta kasheOfishin yaɗa labarai na hukumomin Gaza ya bayyana cewa ana matuƙar buƙatar kayan abincin domin ceto rayuwar musamman ƙananan yara da gajiyayyu da marasa lafiya.
Sanarwar Hukumar ta ce, “laifin yaƙi ne da tauye haƙƙin ɗan Adam ne abin da Isra’ila ke yi na amfani da salon hana faren hula samun abinci a matsayin makami.
“Wannan ya saɓa da yarjejeniyar Geneva da kuma dokokin ayyukan jinƙai na duniya.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tirela ta afka cikin kasuwa ta kashe mutum da raunata 5 a Taraba
Aƙalla mutum ɗaya ne aka tabbatar da mutuwarsa tare da wasu biyar suna jinya bayan da wata babbar mota ƙirar tirela ta ƙwace ta kutsa cikin kasuwar Mile Six da ke Jalingo babban birnin Jihar Taraba.
Shaidun gani da ido a wurin sun bayyana cewa, duk ƙoƙarin da direban motar ya yi na hana afkuwar lamarin ya ci tura.
Ƙudan zuma ya tarwatsa ɗaliban da ke jarrabawar NECO ’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a GombeAƙalla motoci biyu ne suka yi mummunan lalacewa a lamarin.
Jami’an Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) da hukumar tsaro ta farin kaya sibil defens (NSCDC) da kuma rundunar ’yan sandan Najeriya (NPF) sun halarci wurin da jajantawa yankin tare da kawar da ababen hawa don kaucewa sake aukuwar lamarin.
Ɗaya daga cikin manyan motocin da suka tunkari wurin domin wucewa ta hanyar an yi ta jifan su da duwatsu.
Wannan dai shi ne ibtila’i na biyu da ya shafi manyan motocin dakon kaya a yankin inda na farko wata tankar dizal ce wanda ya zube bayan ta faɗi.
An dai ga wasu mutanen da ke wurin suna kuka yayin da wasu kuma suka ɗora alhakin faruwar lamarin a kan rashin ingantattun birki na motoci da ke kan hanyar zuwa kasuwar.