Aminiya:
2025-06-30@17:55:58 GMT

Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran

Published: 30th, June 2025 GMT

Hukumomin Iran sun bayyana cewa aƙalla mutum 935 ne suka rasa rayukansu a hare-haren Isra’ila yayin yaƙin kwanaki 12 da ya gudana tsakaninsu da ƙasar.

Cikin waɗanda suka mutu sun haɗa har da mata 132 da yara 38, kamar yadda mai magana da yawun Hukumar Shari’a, Asghar Jahangir, ya bayyana a wata sanarwa a ranar Litinin, wacce kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ruwaito.

Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe HOTUNA: Sabon shugaban rikon APC APC ya jagoranci taron Majalisar Gudanarwa

A baya, Ma’aikatar Lafiya ta ce adadin wadanda suka mutu sakamakon hare-haren Isra’ila ya kai 606, sannan mutane 5,332 da suka jikkata.

Jahangir ya ce hare-haren Isra’ila kan gidan yari na Evin da ke Arewa maso Yammacin Tehran sun yi sanadin mutuwar mutum 79, ciki har da fursunoni da ma’aikatan gidan yari, da mazauna yankin.

Ya kara da cewa gidan yarin Evin ya zama ba zai iya aiki ba, kuma an kwashe fursunonin, yana mai kiran harin a matsayin “tauye hakkin ɗan’adam da kuma karya dokokin kasa da kasa.”

A ranar 13 ga watan Yunin nan ne yaƙi ya tsakanin Isra’ila da Iran ya barke, lokacin da Tel Aviv ta ƙaddamar da hare-haren sama kan sansanonin soja, nukiliya, da fararen hula na Iran.

Amurka ma ta kai hari kan cibiyoyin nukiliya na Fordow, Natanz, da Isfahan na Iran, wanda ya ƙara tsananta rikicin.

Tehran ta mayar da martani ta hanyar harba makamai masu linzami da jiragen yaƙi marasa matuƙa kan Isra’ila, inda suka kashe aƙalla mutane 29 tare da jikkata fiye da 3,400, kamar yadda Jami’ar Hebrew ta Jerusalem ta bayyana.

Kafofin watsa labarai sun ruwaito cewa yaƙin ya tsaya sakamakon wata yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka ta dauki nauyi, wacce ta fara aiki a ranar 24 ga Yuni.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran Isra ila yaƙi hare haren Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Tirela ta afka cikin kasuwa ta kashe mutum da raunata 5 a Taraba

Aƙalla mutum ɗaya ne aka tabbatar da mutuwarsa tare da wasu biyar suna jinya bayan da wata babbar mota ƙirar tirela ta ƙwace ta kutsa cikin kasuwar Mile Six da ke Jalingo babban birnin Jihar Taraba.

Shaidun gani da ido a wurin sun bayyana cewa, duk ƙoƙarin da direban motar ya yi na hana afkuwar lamarin ya ci tura.

Ƙudan zuma ya tarwatsa ɗaliban da ke jarrabawar NECO ’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe

Aƙalla motoci biyu ne suka yi mummunan lalacewa a lamarin.

Jami’an Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) da hukumar tsaro ta farin kaya sibil defens (NSCDC) da kuma rundunar ’yan sandan Najeriya (NPF) sun halarci wurin da jajantawa yankin tare da kawar da ababen hawa don kaucewa sake aukuwar lamarin.

Ɗaya daga cikin manyan motocin da suka tunkari wurin domin wucewa ta hanyar an yi ta jifan su da duwatsu.

Wannan dai shi ne ibtila’i na biyu da ya shafi manyan motocin dakon kaya a yankin inda na farko wata tankar dizal ce wanda ya zube bayan ta faɗi.

An dai ga wasu mutanen da ke wurin suna kuka yayin da wasu kuma suka ɗora alhakin faruwar lamarin a kan rashin ingantattun birki na motoci da ke kan hanyar zuwa kasuwar.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe ubangidan Turji, Kacalla Ɗanbokolo a Zamfara
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya
  • Falasdinu: Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Yammacin Kogin Jordan
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta da Isra’ila ta kashe
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta Isra’ila ta kashe
  • Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe
  • Tirela ta afka cikin kasuwa ta kashe mutum da raunata 5 a Taraba