Aminiya:
2025-11-27@22:28:38 GMT

‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’

Published: 3rd, July 2025 GMT

’Yan Majalisar Wakilai daga jihohin Neja da Kwara sun shaida wa majalisar cewa mutum 600 da suka bace a ambaliyar garin Mokwa kuma har yanzu ba a gan su ba, za a dauka su ma sun mutu.

Dan majalisa Joshua Audu Gana (Neja) da Saba Ahmed Umaru (Kwara) ne suka bayyana hakan a yayin gabatar da wani kudurin gaggawa a zauren majalisar a ranar Laraba.

Sun ce mummunar ambaliyar da aka yi a ranakun 28 da 29 ga watan Mayun da ya gabata sanadin mamakon ruwan saman da aka tafka ta yi barna sosai a karamar hukumar ta Mokwa a jihar Neja, sannan ta tsallaka har karamar hukumar Edu ta jihar Kwara.

Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta

A cewar ’yan majalisar, yayin da aka tabbatar da mutuwar mutum 500, su kuma ragowar sama da 600 da aka ce sun bace kuma har yanzu babu labarin su, su ma za a kirga su a cikin matattun, la’akari da munin ambaliyar.

’Yan majalisar sun kuma ce ambaliyar ta lalata gidaje sama da 4,000, ta jikkata sama da mutum 200, sannan ta shanye gonaki da gine-gine, ta kuma raba dubban mutane da muhallansu.

Daga nan ne majalisar ta yi shiru na minti daya don girmama wadanda ambaliyar ta shafa, sannan ta yaba wa Shugaban Kasa Bola Tinubu saboda amincewa a bayar da tallafin Naira biliyan biyu ga wadanda lamarin ya shafa.

Majalisar, bayan tafka muhawara, ta kuma amince da kudurin sannan ta ba da umarnin inganta matakan dakile ambaliya a yankin da ma sauran yankunan da ke cikin barazanar ambaliyar, cikin gaggawa.

Kazalika, majalisar ta kuma umarci Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) da ta samar da kayayyakin agaji da na tsafta ga al’ummomin da lamarin ya shafa domin kaucewa sake barkewar cututtuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliya Mokwa

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu

Shugaba Bola Tinubu ya aike da sunan mutum uku zuwa Majalisar Dattawa, domin tantance su a matsayin sabbin jakadan Najeriya.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne, ya sanar da haka a zaman majalisar na ranar Laraba.

Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna

Waɗanda aka zaɓa su haɗa da Kayode Are daga Jihar Ogun, Aminu Dalhatu daga Jihar Jigawa da kuma Ayodele Oke.

Bayan karanta takardar Tinubu, Akpabio ya ce, “Sunaye uku ne zuwa yanzu, tabbas sauran za su biyo baya.”

Tun bayan ɗarewarsa kan mulki a 2023, Tinubu bai naɗa jakadu ba har yanzu.

Mutane da dama sun daɗe suna ƙorafin kan jinkirin naɗa jakadun.

Amma wasu na ganin aike sunayen jakadun na da alaƙa da barazanar da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na ɗaukar matakin soji a kan Najeriya, kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

A wata hira da aka yi da shi a watan Satumba, Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar, ya ce babu wata matsala game da jinkirin.

Ya ce, “Dukkanin ofisoshin jakadancinmu suna aiki yadda ya kamata. Kowace ofishi yana gudanar da ayyukansa yadda ya dace. Rashin jakadu ba zai haifar da giɓi ba.”

Ya ƙara da cewa duk da cewa jakada shi ne shugaban ofishin jakadanci, akwai kwamishinoni, wakilai da ma’aikatan diflomasiyya da ke tafiyar da harkokin yau da kullum.

A cewarsa, “Diflomasiyya ba aikin mutum ɗaya ba ne. Tsarin ya tanadi irin wannan yanayi.”

Tuggar, ya kuma ce shugaban ƙasa ne kaɗai ke da ikon naɗa jakadu, kuma zai yi hakan a lokacin da ya dace.

Ya bayyana cewa, “Shugaban ƙasa yana duba batun, kuma za a sanar da sunayen a lokacin da ya dace.”

Ya ƙara da cewa, “’Yan Najeriya a ƙasashen waje har yanzu suna samun ayyuka, kuma mu’amala da ƙasashen da muke hulɗa da su ba ta ragu ba.”

Ya ce kuma akwai ƙasashe da dama da suka shafe dogon lokaci ba tare da jakadu ba, amma hakan bai lalata dangantakarsu da wasu ƙasashe ba.

Ya ce, “Wannan ba sabon abu ba ne. Diflomasiyya tana da tanadin irin wannan yanayi. Abin da ya fi muhimmanci shi ne aiki, ba kwaikwayo ba.”

A ƙarshe ya ce Najeriya tana aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran ƙasashen duniya.

“Manufofin ƙasashen waje na Najeriya sun bayyana, kuma ana jinmu a duniya. Abin da muke yi shi ne tabbatar da cewa ofisoshinmu suna samar da sakamako mai amfani ga ’yan Najeriya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • ’Yan bindiga sun yi yi garkuwa da mutane 11 a Kwara
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja