Aminiya:
2025-07-03@11:10:59 GMT

‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’

Published: 3rd, July 2025 GMT

’Yan Majalisar Wakilai daga jihohin Neja da Kwara sun shaida wa majalisar cewa mutum 600 da suka bace a ambaliyar garin Mokwa kuma har yanzu ba a gan su ba, za a dauka su ma sun mutu.

Dan majalisa Joshua Audu Gana (Neja) da Saba Ahmed Umaru (Kwara) ne suka bayyana hakan a yayin gabatar da wani kudurin gaggawa a zauren majalisar a ranar Laraba.

Sun ce mummunar ambaliyar da aka yi a ranakun 28 da 29 ga watan Mayun da ya gabata sanadin mamakon ruwan saman da aka tafka ta yi barna sosai a karamar hukumar ta Mokwa a jihar Neja, sannan ta tsallaka har karamar hukumar Edu ta jihar Kwara.

Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta

A cewar ’yan majalisar, yayin da aka tabbatar da mutuwar mutum 500, su kuma ragowar sama da 600 da aka ce sun bace kuma har yanzu babu labarin su, su ma za a kirga su a cikin matattun, la’akari da munin ambaliyar.

’Yan majalisar sun kuma ce ambaliyar ta lalata gidaje sama da 4,000, ta jikkata sama da mutum 200, sannan ta shanye gonaki da gine-gine, ta kuma raba dubban mutane da muhallansu.

Daga nan ne majalisar ta yi shiru na minti daya don girmama wadanda ambaliyar ta shafa, sannan ta yaba wa Shugaban Kasa Bola Tinubu saboda amincewa a bayar da tallafin Naira biliyan biyu ga wadanda lamarin ya shafa.

Majalisar, bayan tafka muhawara, ta kuma amince da kudurin sannan ta ba da umarnin inganta matakan dakile ambaliya a yankin da ma sauran yankunan da ke cikin barazanar ambaliyar, cikin gaggawa.

Kazalika, majalisar ta kuma umarci Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) da ta samar da kayayyakin agaji da na tsafta ga al’ummomin da lamarin ya shafa domin kaucewa sake barkewar cututtuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliya Mokwa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Kasar Sin ta kawo karshen aikin bayar da agajin gaggawa mafi girma a gundumar Rongjiang da ke lardin Guizhou, a yankin kudu maso yammacin kasar da misalin karfe 10 na safiyar ranar Lahadi, yayin da aka kammala ruwan saman da aka tafka kamar da bakin kwarya kamar yadda mahukuntan yankin suka bayyana.

Lardin Guizhou da wasu larduna masu iyaka da shi da ke kudu maso yammacin kasar Sin sun fuskanci mamakon ruwan sama tun daga ranar 18 ga watan Yuni, lamarin da ya haifar da mummunar ambaliyar ruwa, inda lamarin ya fi muni a yankin Rongjiang.

Mahukuntan yankin sun raba yankin zuwa kashi bakwai a matsayin wadanda ambaliyar ta fi shafa tare da kwashe mazauna zuwa wasu manyan wurare masu tudu. An kwashe fiye da mutane 40,000 zuwa wurare masu aminci tun karfe 6 na yammacin ranar Asabar saboda rigakafin hadarin ambaliyar.

Kasar Sin ta ware karin kudi yuan miliyan 100, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 13.96 daga cikin kasafin kudin gwamnatin tsakiya don tallafa wa ayyukan ba da agajin gaggawa da farfado da lardin Guizhou da ambaliyar ruwan ta shafa, inda hakan ya kara adadin kudin da aka ware zuwa yuan miliyan 200, kamar yadda hukumar raya kasa da gudanar da gyare-gyare ta kasar ta bayyana. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato
  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata 2 bayan ambaliya
  • Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran