Iran Ta Ce: Ba Za Ta Koma Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Sai A Kan Wasu Sharudda
Published: 30th, June 2025 GMT
Dakatar da ayyukan wuce gona da iri kan Iran wani sharadi ne na ci gaba da tattaunawar makamashin nukiliya
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran mai kula da harkokin siyasa Majid Takht-e Ravanchi ya bayyana cewa: Sharadin ci gaba da gudanar da zaman shawarwarin makamashin nukiliyar Iran shi ne dakatar da duk wani matakin wuce gona da iri kan Iran, kuma har yanzu Amurka ba ta dauki wani mataki ba kan wannan batu.
A wata hira da tashar BBC game da batun tattaunawar makamashin nukiliyar Iran da Amurka: Takht-e Ravanchi ya ce: “Sun ji daga Amurka cewa a shirye take ta ci gaba da tattaunawar, amma har yanzu ba a tsayar da ranar ba, kuma Iran ba ta amince da tsarin shawarwarin ba.”
Ya kara da cewa: “A halin yanzu Iran tana neman amsoshi dangane da ko za ta sake fuskantar sabbin matakan wuce gona da iri yayin da aka fara tattaunawar.” Har yanzu dai Amurka ba ta bayyana matsaya ba kan wannan batu.
Da aka tambaye shi game da yiwuwar cimma yarjejeniya tsakanin bangarorin biyu, ciki har da dage takunkumin da aka kakabawa Iran, a madadin Iran ta dakatar da inganta sinadarin Uranium, Takht-e Ravanchi ya ce: “Me zai sa su amince da wannan shawara? Inganta sinadarin Uranium zuwa kashi 60 cikin 100 ana amfani da shi ne domin zaman lafiya. Tabbas za a iya tattaunawa kan matakinsa, amma maganarsu ta cewa dole ne Iran ta daina inganta Uranium gaba daya, in ba haka ba za ta fuskanci hari, wannan maganar hankali me? Wannan dokar daji ce.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Babu Wani Alfanu A Ci Gaba Da Bai Wa IAEA Hadin Kai
Kwamitin koli na tsaron kasa a cikin majalisar shawawar musulunci ta Iran ya bayyana cewa; Saboda yadda hukumar makamashin Nukiliya ta kasa da kasa ( IAEA) take ci gaba da siyasarta na nuna wariya, ci gaba da aiki da ita ba shi da wani alfanu a wurin Iran.
Shugaban kwamitin tsaron kasar a majalisar shawarar musulunci ta Iran Ibrahim Azizi ya bayyana cewa; Karkataccen rahoton da hukumar makamashin Nukiliyar ta kasa da kasa ya gabatar ne ya zama abinda HKI ta fake da shi wajen kawo wa Iran hari na ta’addanci.
Azizi ya kara da cewa; Iran ta sha nanata cewa, shirinta na Nukiliya na zaman lafiya ne, kuma yana gudana ne a karkashin yarjejeniyar hana yaduwar makaman Nukiliya.
Ibrahim Azizi ya kuma kara da cewa; A lokuta da dama Iran ta karbi bakuncin shugaban hukumar makamashin Nukiliyar ta kasa da kasa Grossy, ya kuma ziyarci cibiyoyin makamashin Nukiliya; amma wannan hukumar ta daina aiki da ilimi da kwarewa ta koma abin wasa a hannun manyan kasashe.
Haka nan kuma ya ce; Saboda yadda hukumar ta koma aiki da siyasar nuna wa Iran wariya, ci gaba da yin aiki da ita ba shi da wani alfanu ga Iran.