Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci
Published: 1st, July 2025 GMT
Yau Talata da safe, shugaban kasar Sin, kana babban darektan kwamitin harkokin kudi da tattalin arziki na kwamitin tsakiyar Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, Xi Jinping ya jagoranci taro karo na 6 na kwamitin harkokin kudi da tattalin arziki na kwamitin tsakiyar JKS, inda aka yi nazari kan yadda za a gina babbar kasuwar kasa ta bai daya, tare da raya tattalin arziki na teku mai inganci da dai sauransu.
A yayin taron, shugaba Xi ya jaddada cewa, kafuwar babbar kasuwa ta bai daya a ciki kasar Sin ta dace da bukatunmu na bullo da sabon tsarin neman ci gaba da samun bunkasa mai inganci, don haka ya kamata a aiwatar da aikin bisa manufar kwamitin tsakiya, da daidaita ayyuka yadda ya kamata, domin cimma burinmu cikin hadin gwiwa.
Haka kuma, ya ce, ya kamata a inganta bunkasa tattalin arziki na teku kamar yadda ake bukata domin ciyar da zamanantarwar kasar Sin gaba, tare da neman hanyar raya kasa ta teku bisa yanayin da kasar Sin take ciki. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tattalin arziki na
এছাড়াও পড়ুন:
Kuri’ar Jin Ra’ayi Ta CGTN: Ya Kamata Japan Ta Martaba Tarihi
A yau Juma’a ne kasar Japan ta gudanar da gangamin tunawa da wadanda suka rasa rayukansu yayin yakin duniya na biyu, sai dai yayin da yake jawabi albarkacin taron, firaministan kasar Shigeru Ishiba, bai tabo batu kan alhakin dake rataye a wuyan kasarsa ba, a matsayinta na wadda ta mamayi wasu kasashen nahiyar Asiya. A hannu guda kuma ya gabatar da addu’a ga wurin ibadar nan na Yasukuni, a matsayin girmmawa ga wurin ibadar da ake kallo a matsayin wurin da aka karrama mutanen da suka tafka danyen aiki yayin yakin duniya na biyu. Kazalika, wasu ministocin kasar sun kaiwa wurin ibadar na Yasukuni ziyarar girmamawa.
Jerin wadannan matakai dai na shan suka, da adawa daga sassan kasa da kasa. Inda wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar game da hakan ta nuna cewa, kaso 64.4 bisa dari na masu bayyana ra’ayin na adawa da ziyarar ‘yan siyasar na Japan zuwa wurin ibadar. Kana kaso 55.3 bisa dari sun soki lamirin Japan bisa yadda ta kawar da kai daga abun da ya auku na tarihin wurin. Kazalika, kaso 65.2 bisa dari sun soki matakin Japan na sauya bayanai dake kunshe cikin litattafan tarihi masu nasaba da batun. Sai kuma kaso 65.7 bisa dari da suka yi kira ga gwamnatin Japan da ta nemi afuwar kasashen da mamayarta ta cutar tare da biyansu diyya.
Wannan dai batu ya haifar da bayyana matukar rashin jin dadi tsakanin al’ummun nahiyar Asiya, ciki har da al’ummun Koriya ta Kudu, da sukarsu game da hakan ya haura kaso 90 bisa dari. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp