Leadership News Hausa:
2025-10-13@15:49:44 GMT

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Published: 2nd, July 2025 GMT

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Shugabannin jam’iyyar APC a matakin gunduma na Gayam, cikin ƙaramar hukumar Lafia, sun dakatar da shugaban jam’iyyar a matakin jiha, Hon. Aliyu Bello. Sun zarge shi da aikata abubuwan da suka saɓa da kundin tsarin mulki na jam’iyyar, musamman sashe na 21 (D)(i–iii), wanda ya haɗa da cin amanar jam’iyya da goyon bayan ɗan takarar wata jam’iyya daban.

Shugaban gundumar, Ibrahim Ilyasu, ya bayyana cewa matakin dakatarwar ya fara aiki nan take, kuma Hon. Bello ba zai iya wakiltar kansa ko amfani da matsayin sa a matsayinsa na mamba na APC daga Gayam ba, har sai an warware batutuwan da aka gabatar. Sun kuma zarge shi da jawo wa jam’iyyar tozarci da keta mutuncinta a idon jama’a.

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A Kano

Sai dai wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyar a jihar sun ce wannan matakin wani yunkuri ne daga wani ɓangare na ƙungiyar siyasa da ke ƙoƙarin kifar da Bello daga kujerarsa, musamman bisa alaƙa da wani ɗan takarar gwamna a jihar. Sun ce wannan rikici ya ƙara bayyana rabuwar kai da rikicin cikin gida a jam’iyyar.

A wata ganawa da wasu shugabannin jam’iyyar a Lafia, an kaɗa ƙuri’ar nuna goyon baya da amincewa da shugabancin Hon. Bello, wanda hakan ke nuna cewa har yanzu akwai sassa a jam’iyyar da ke goyon bayansa, duk da dakatarwar da aka sanar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nassarawa a jam iyyar jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

Ya ci gaba da bayanin cewa, “Da zan koma Kaduna sai ya ba ni takarda na kai wa Wazirin Katsina, Alhaji Isa Kaita. Na zo Kaduna na yi jarrabawa, bayan mun kare na koma gida ina sauraren sakamakon jarrabawar. Ba zan taba mantawa ba, ana zaune wajen Hawan Daba don tarbar Sarauniyar Ingila sai na sami telegiram mai cewa na ci jarrabawa ana nema na a Kaduna.

 

“Na fadawa mahaifina. Muka kintsa muka bar Katsina sai Kaduna, daga Kaduna muka tafi Legas. Da isa ta Legas sai na ga abokan nawa da suka sami nasarar wannan tafiyar duk ‘yan Kudu ne. Ni kadai ne dan Arewa kuma Bahaushe cikin daga cikin mu takwas

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique October 11, 2025 Daga Birnin Sin Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia October 11, 2025 Daga Birnin Sin Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Ba Bu Dalilin Da ASUU Za Ta Fara Yajin Aiki, An Biya Duk Buƙatunsu – Ministan Ilimi 
  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Ƴan Bindiga Sun Amince Da Dakatar Da Hare-Hare A Ƙananan Hukumomi 5 A Katsina
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Tarihin Hassan Usman Katsina (1)
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza