Bincike Ya Tabbatar da Cewa HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 Tun Bayan Fara Yaki A Gaza
Published: 29th, June 2025 GMT
Masu bincike sun gano cewa sojojin HKI sun kashe Falasdinawa akalla 100,000 tun bayan fara yakin tufanul Aksa a ranar 7 ga watan Octoban shekara 2023.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kan cewa farfesa Michael Spagat da kuma Khalil Shikaki Bafalasdine masanin masanin fasahar siyasa a Jami’ar London na kasar Burtania suka jagoranci bincike wanda ya kai ga fitar da wannan sakamakon.
Labarin ya kara da cewa masu binciken sun kiyasta mutane a gidaje 2000 a birnin Gaza kadai wanda falasdinawa kimani 10,000 suke rayuwa, sannan suka yi lissafi suka kaim ga wannan sakamakon.
Bincike ya kara da cewa daga watan jenerun shekara ta 2025 falasdinawa 75,200 sojojin yahudawan suka kashe da makamai, sannan wasu kimani 8,540 sun mutu sabada yunwa da karancin magunguna da kuma wasu hanyoyi ba da wuta ba.
Amma ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta bayyana cewa daga watan Jeneru zuwa yanzu sojojin yahudawan sun kashe falasdinawa 10,000.
Ma’aikatar ta kara da cewa a baya bayan nan sojojin yahudawa suna kashe Falasdinawa a wuraren karban abinci da suka shirya a matsayin tarko ga Falasdinawa wadanda suke fama daga tsananin yunwa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kashe Falasdinawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Alhaji Ahmad Manga ya ce, “an ɗauki matakin ne da haɗin gwiwar gwamnatin jiha da gwamnatin tarayya”.
Jami’an CPG na Zamfara sun kuma samu goyon bayan dakarun Civilian JTF na jihar Borno, inda suka ƙaddamar da harin a-yi-ta-ta-ƙare na bazata ga maɓoyar ta Bello Turji.
Gwamnatin jihar Zamfara ta ce artabun na ranar Litinin da haɗin gwiwar jami’an tsaro suka fara da ɗan fashin dajin tamkar buɗe sabuwar ƙofar ci gaba da yaƙarsa ne.
“Alhamdulillahi an tarar da shi har gida nai inda ba a taɓa zuwa ba, kuma ya ga cewa ana iyawa, kuma an isko shi,” inji Ahmad Manga.
Ya ƙara da cewa “an kuma buga wuta, an yi nasarori da dama inda aka kashi mutanensa, wanda shi kansa bai iya ƙididdige abin da ya rasa, sai dai daga baya”.
Ya ce duk inda ka ga gawawwaki to akasari na yaransa ne.
Mataimaki na musamman kan sha’anin tsaron ya ce Bashari Maniya ya gamu da ajalinsa ne sakamakon hatsarin da motarsu ta yi lokacin da ta faɗa wani rami.
“Sabuwar mota ce wanda ba duk mutum ya san kanta ba, sun taka wani rami ne mai kama da rijiya kuma suna a guje, motar ta ƙwace kuma ta je ta faɗi. Ba wai shi ne ya yi nasarar buge motar ba, a’a.”
Ya ƙara da cewa lokacin da aka kai musu ɗauki an samu Maniya da sauran waɗanda ke cikin motar ne ba a hayyacinsu ba, saboda motar harbi ba ya ratsa ta.
Alhaji Ahmad Manga ya ba da tabbacin cewa gwamnatin jihar Zamfara za ta ci gaba da farautar Bello Turji ba rdare ba rana.
“Wallahi sai abin da ya ci gaba. Alhamdulillahi! Duk ɗan jihar Zamfara zai gaya maka musamman ɗan yankin Shinkafi sun sani, abin da aka yi shekara 14 yana gallaza wa mutane. Shi ya san rawar da jami’an tsaro suka taka yanzu ba a taɓa isko shi ba, irin yadda aka tarad da shi har gidansa.
Ya bayyana aniyar gwamnatin Zamfara na shigo da ƙarin dakarun sojoji don ci gaba da tunkarar Bello Turji
A cewarsa, ko a faɗan da aka yi ranar Litinin Bello Turji laɓewa ya riƙa yi, kafin daga bisani ya arce.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp