An Hori Ma’aikatan Lafiya Su Kara Kokari Wajen Rike Aikin su
Published: 3rd, July 2025 GMT
Shugaban hukumar kula da makarantun kiwon lafiya da bada lasisi ga likitoci kula da lafiya a matakin farko ta kasa Alhaji Dr Bashir Idiris Lifidin Jama’a ya hori ma’aikatan kiwon lafiya a matakin farko da dukkannin masu ruwa da tsaki a bangaren lafiya su rubanya kokari fuskar tabbatar da kwarewa domin inganta ayyukan kula da lafiya a Nijeriya.
Dr. Bashir Idiris Lifidin Jama’a ya yi wannan kiran ne a Katsina lokacin bukin rufe taron karawa juna sani na tsawon kwanaki uku na wannan shekarar wanda aka shiryawa Malaman koyar da darusan kiwon lafiya a matakin farko.
Taron wanda ya samu halartan jami’an kiwon lafiya daga dukkannin jihohin yankin arewa maso yamma, yana da nufin ilimintar dasu ne kan yadda za su rungumi sabbin dabarun aiki irin na zamani dai dai da tsarin dokokin hukumar kula da makarantun kiwon lafiya da bada lasisi ga likitocin kula da lafiya a matakin farko ta Naheriya.
Dr. Bashir Idiris Lifidin Jama’a ya bayyana cewa wajibi ne dukkannin ma’aikatan hukumar da sauran masu ruwa da tsaki a bangaren lafiya a matakin farko su kara zama masu kwazo tare da yin aiki da sauran dokokin aiki na fasahohin zamani domin kwalliya ta biya kudin sabulu.
Don haka shugaban hukumar ya sake yin kira ga malarta taron su yi amfani da abubuwan da suka koya yadda suka dace domin bunkasa harkokin kiwon lafiya a Naheriya.
Maryam Idris
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jami an Lafiya lafiya a matakin farko kiwon lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana cewa: Iran tana goyon bayan duk wani Shirin zaman lafiya da ya hada da dakatar da kisan kiyashi a Gaza
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta tabbatar da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana goyon bayan duk wani mataki ko wani yunkuri da ya hada da kawo karshen yakin kisan kiyashi a Gaza, janyewar sojojin mamayar Isra’ila, shigar da kayan agajin jin kai, sakin fursunonin Falastinawa, da kuma tabbatar da dukkanin hakkokin Falasdinawa.
Haka kuma ta kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran a matsayinta na mai goyon bayan halastacciyar gwagwarmayar al’ummar Falastinu samun tabbatar da ‘yancin kai, ta yi amfani da dukkanin karfinta na diflomasiyya a cikin shekaru biyun da suka gabata, musamman a matakin yanki, kungiyar hadin kan kasashen musulmi, da Majalisar Dinkin Duniya, wajen matsin lamba ga yahudawan sahayoniyya da magoya bayansu da su dakatar da kisan kiyashi da kuma janyewar ‘yan mamaya daga Gaza.
Ma’aikatar harkokin wajen kasar ta yi juyayin tunawa da manyan shahidan gwagwarmaya, inda ta jaddada nauyin da ke wuyan kasashen duniya na hana duk wani cin zarafi daga ‘yan mamaya, tare da yin kira ga dukkan bangarorin da su yi taka tsantsan da yaudara da karya alkawari da sahayoniyya suke yi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran October 11, 2025 Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya October 11, 2025 Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta October 11, 2025 Putin: Natanyahu Yana Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba October 10, 2025 Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha October 10, 2025 Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa October 10, 2025 Falasdinawa Daga Kudancin Gaza Sun Fara Komawa Gidajensu Da Aka Rusa A Arewacin Yankin October 10, 2025 Rahotanni : Isra’ila ta fara janye dawa wasu yankuna na Gaza October 10, 2025 Amurka ta kakaba wa wasu kamfanoni 50 takunkumi saboda sayen man Iran October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci