Darakta Janar Na Hukumar IAEA Ya Ce; Babu Tabbas Iran Na Da Shirin Mallakar Makamin Nukiliya
Published: 28th, June 2025 GMT
Darakta Janar na hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA ya bayyana cewa: Ba zai iya tabbatar da cewa Iran na kera makamin nukiliya ba!
A wata hira da tashar talabijin ta Faransa LCI, Darakta Janar na hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA Rafael Grossi ya bayyana cewa: Ba zai iya tabbatar da cewa Iran tana kera makamin nukiliya ba.
Grossi dai ya fuskanci tambayoyi da kalubale da dama daga mai gabatar da Shirin, kan ko Iran na daf da kera makamin nukiliya? Ya amsa a cikin halin shakku, yana mai cewa a cikin rahoton ya nisanci zargin Iran da kokwarin kera makamin nukiliya domin babu tabbas kan zargin.
Da aka tambaye shi ko Iran na kera makamin nukiliya? Grossi ya amsa da cewa: “Ba zai iya tabbatar da hakan ba, kuma zai zama rashin gaskiya idan aka ce suna shirin kera makamin nukiliya.”
Da yake amsa tambayar da mai gabatar da shirin ya yi danganr da wasu masu kallon Shirin suna kokwanton ingancin harin da aka kai kan Iran: Grossi ya kare hare-haren wuce gona da irin haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka kan cibiyoyin nukiliyar Iran, da ba su kan ka’ida, yana mai cewa akwai yanayi na uku a cikin dabarun kera makamin nukiliya da ake kira “boyayyen shiri” ko “shirin da bai fito fili ba” inda har yanzu Shirin bai kai matakin kera makamin ba, amma ta mallaki dukkan karfin iko da fasahohin da ake bukata, kuma idan lokaci ya yi, za su iya mallaka. Ya kara da cewa Iraniyawa suna da fatawar haramta mallakar makamin nukiliya da sauran makaman kare dangi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kera makamin nukiliya
এছাড়াও পড়ুন:
Arakci: Idan Aka Kai Iran Bango Za Ta Fito Da Hakikanin Karfin Da Take Da Shi
Minsitan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci ya kira yi shugaban kasar Amurka Donald Ttump da ya daina yin maganganun da ba su dace ba akan jagoran juyin musulunci Ayatullah sayyid Ali Khamnei.
Abbas Arakci ya kara da cewa; Ko kadan Tehran ba za ta bari wani mahaluki ya ayyana mata makoma ba, idan kuwa har aka kai ta bango ta za ta bayyana hakikanin karfin da take da shi.
A jiya Juma’a ne dai shugaban kasar ta Amurka ya yi maganganu na rashin labadi akan jagoran juyin musulunci, sannan kuma ya kara da cewa, zai sake kawo wa Iran hari idan ta koma tace sanadarin uranium.
Jamhuriyar musulunci ta Iran dai ta sha jaddada cewa ba za ta ja da baya ba akan hakkinta na tace sanadarin Uranium da cin moriyar fasahar Nukiliya ta hanyoyin zaman lafiya.
Arakci ya kuma ce; Idan har shugaban kasar ta Amurka da gaske yake akan batun tattaunawa da kai wa ga cimma wata yarjejeniya, to ya daina yin Magana da harshe na rashin ladabi akan jagoran juyin musulunci.