Darakta Janar na hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA ya bayyana cewa: Ba zai iya tabbatar da cewa Iran na kera makamin nukiliya ba!

A wata hira da tashar talabijin ta Faransa LCI, Darakta Janar na hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA Rafael Grossi ya bayyana cewa: Ba zai iya tabbatar da cewa Iran tana kera makamin nukiliya ba.

Grossi dai ya fuskanci tambayoyi da kalubale da dama daga mai gabatar da Shirin, kan ko Iran na daf da kera makamin nukiliya? Ya amsa a cikin halin shakku, yana mai cewa a cikin rahoton ya nisanci zargin Iran da kokwarin kera makamin nukiliya domin babu tabbas kan zargin.

Da aka tambaye shi ko Iran na kera makamin nukiliya? Grossi ya amsa da cewa: “Ba zai iya tabbatar da hakan ba, kuma zai zama rashin gaskiya idan aka ce suna shirin kera makamin nukiliya.”

Da yake amsa tambayar da mai gabatar da shirin ya yi danganr da wasu masu kallon Shirin suna kokwanton ingancin harin da aka kai kan Iran: Grossi ya kare hare-haren wuce gona da irin haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka kan cibiyoyin nukiliyar Iran, da ba su kan ka’ida, yana mai cewa akwai yanayi na uku a cikin dabarun kera makamin nukiliya da ake kira “boyayyen shiri” ko “shirin da bai fito fili ba” inda har yanzu Shirin bai kai matakin kera makamin ba, amma ta mallaki dukkan karfin iko da fasahohin da ake bukata, kuma idan lokaci ya yi, za su iya mallaka. Ya kara da cewa Iraniyawa suna da fatawar haramta mallakar makamin nukiliya da sauran makaman kare dangi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kera makamin nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano

 

Sanarwar ta kara da cewa, “mun yi farin cikin ganin cewar yan wasan kungiyoyin biyu da jami’an wasan duk sun bar filin wasan ba tare da samun wani rauni ba kuma jami’an tsaro suka yi musu rakiya, kungiyar ta kara da cewa an kama wasu da dama da ake zargi da hannu a rikicin tare da mika su ga hukumomin tsaro domin gudanar da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.

 

Kungiyar ta jaddada kudirinta na tabbatar da zaman lafiya da da’a, kungiyar ta jaddada cewa za ta ci gaba da tabbatar da ingancin wasan kamar yadda hukumar NPFL da hukumar kwallon kafar Najeriya NFF ta tanada, Pillars ta kuma yi kira ga magoya bayanta da su gudanar da ayyukansu cikin lumana tare da ci gaba da ba kungiyar goyon baya, amma kuma wani bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta ya nuna yan wasan 3SC da aka jikkata tareda raunuka a jikinsu.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or? October 12, 2025 Wasanni Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka October 12, 2025 Wasanni Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • An Kara Zaburar Da ‘Yan Arewa Game Da Muhimmancin Mallakar Katin Zabe
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
  • Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
  • Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano