David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
Published: 2nd, July 2025 GMT
Aregbesola, wanda shi ne tsohon Gwamnan Jihar Osun, ya ƙara da cewa jam’iyyar siyasa bai kamata ta zama hanyar neman mulki kawai ba ko wata dama ga wasu tsiraru ba.
Ya ce jam’iyya ta gaskiya ita ce wadda ke da tsari da manufa, kuma wadda ke aiki don jama’ar da ta ke wakilta.
Daga kanmu, magana ta ƙare.
কীওয়ার্ড: Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC na ƙasa ta rasu
Mama Lydia Yilwatda, mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ta rasu.
Mai magana da yawun jam’iyyar APC a Jihar Filato, Shittu Bamaiyi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Jos ranar Lahadi.
Jirgin ruwa ya nutse da mutum 30 a Sakkwato Adam A. Zango ya auri jarumar KannywoodA cewar Bamaiyi, Mama Lydia ta rasu ne da safiyar ranar Lahadi a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos tana da shekaru 83.
Ya ce, rasuwarta babban rashi ne ba ga Shugaban APC kawai ba, har ma da iyalinsa da kuma jam’iyyar APC a Jihar Filato da Najeriya baki ɗaya.
Bamaiyi, ya bayyana Mama Lydia a matsayin mace mai tsantseni wajen ibada, jajirtacciyar shugabar mata a Cocin Christ in Nation.
Ya ce tare da mijinta marigayi Fasto Toma Goshewe Yilwatda sun yi ƙoƙari wajen bunƙasa coci a jihohin Borno, Yobe, Bauchi da Filato.
Ya ƙara da cewa Mama Lydia ta bar tarihi mai kyau ta hanyar gina ’ya’yanta da kuma hidimar da ta yi wa coci da al’umma.
Jam’iyyar ta yi addu’ar Ubangiji Ya jiƙan ta kuma ya bai wa Farfesa Yilwatda da iyalinsa haƙuri da juriyar wannan babban rashi.