Aminiya:
2025-06-14@01:11:20 GMT

An kama ƙasurgumin ɗan bindiga yayin tantance alhazai a Abuja

Published: 18th, May 2025 GMT

Wani mutum da ake nema ruwa a jallo bisa zargin garkuwa da mutane an kama shi a sansanin alhazai da ke Abuja.

Wata majiya daga jami’an tsaro ta tabbatar wa wakilinmu cewa an kama wanda ake zargin, mai suna Yahaya Zango, yayin da ake tantance takardun maniyyatan da ke shirin tafiya Ƙasar Saudiyya domin aikin Hajjin bana.

’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa.Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027?

Rahotanni sun bayyana cewar Zango yana zaune ne a unguwar Paikon-Kore da ke cikin Ƙaramar Hukumar Gwagwalada a Babban Birnin Tarayya, Abuja.

Jami’an tsaro sun bayyana shi a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo saboda zarginsa da hannu wajen garkuwa da mutane.

Majiyar ta ce mutumin ya zo da fasfonsa tare da sauran maniyyatan Abuja, amma jami’an hukumar DSS suka gane shi kuma suka cafke shi nan take suka tafi da shi.

Wani babban jami’i daga hukumar jin daɗin alhazai, ya tabbatar da kama shi, amma ya buƙaci a sakaya sunansa.

Rahotanni sun nuna cewa an daɗe ana nemansa kafin daga bisani aka yi nasarar cafke shi.

Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan Abuja, SP Josephine Adeh, ta ce: “Ka ce DSS ce ta kama shi, amma ni kakakin rundunar ’yan sandan Abuja ce.”

DSS dai ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Kasancewar Najeriya na fama da matsalolin tsaro, hukumomi na ci gaba da ƙoƙarin magance su, duk da cewar har yanzu ana fama da barazanar hare-haren ’yan ta’adda.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Bindiga garkuwa da mutane Tantancewaz DSS

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin

Yayin taron shekara-shekara na tattaunawar CBD na shekarar 2025 da aka rufe a yau Juma’a 13 ga wata, mashawarci kana kwararre a hukumar kasuwancin kasar Sin ta kasar Birtaniya, kuma shugaban cibiyar bunkasa kasuwanci tsakanin Birtaniya da Sin mista John Mclean, ya bayyana yayin da yake hira da wakilin CMG cewa, kasuwar kasar Sin tana cike da damammaki, don haka dole ne ya shiga a dama da shi a cikinta. A ganinsa, yayin da ake tinkarar tashe-tashen hankula da rashin tabbaci a duniya, babbar baiwar da Sin take da ita, da muhalli mai aminci da bude kofa ga kowa, sun samarwa kamfanonin Birtaniya da ma duniya baki daya damammaki.

Tun bayan kafuwarsa a shekarar 2000 zuwa yanzu, taron ya kasance dandali da kasar Sin ke tattaunawa da kasashen duniya. A yayin taron bana, wakilai fiye da 6000 daga sassan siyasa, da kasuwanci, da ilimi da suka fito daga kasashe da yankuna fiye da 40 sun halarta. A lokacin gudanar da taron, wasu mahalartansa sun yi nuni da cewa, kasar Sin na da babbar juriya wajen raya tattalin arziki, da kuma babbar baiwar raya kasa. Haka kuma, gwamnatin Sin ta gaggauta raya sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, lamarin da ya zuba sabon kuzari ga kamfanonin kasashen waje, ta yadda suke shiga a dama da su wajen yin ciniki a kasar Sin.

A yayin bikin bude taron, mahalartansa sun yi kira da a gina duniya mai tsabta, da kyawu, da dorewa cikin hadin gwiwa, duba da ganin kasar Sin ta ba da babbar gudummawa, ta kuma yi iyakacin kokari a fannin raya kasa ba tare da gurbata muhalli ba, da kuma rage fitar da sinadarin carbon. Alkaluma sun nuna cewa, yanzu haka kasar Sin tana daya daga cikin kasashen da suka fi saurin rage yawan makamashi mai dumama yanayi da suke amfani da shi da samun kyautatuwar iska, ta kuma dasa yawan bishiyoyi, da ciyayi da fadinsu ya kai rubu’i bisa jimillar fadin sabbin bishiyoyi da ciyayi na duniya baki daya, tare da kafa tsarin makamashin da ake sake amfani da shi mafi girma, kuma mafi saurin ci gaba a duniya, baya ga kafa tsarin masana’antu na sabbin makamashi mafi girma kuma cikakke a duniya. (Tasallah Yuan)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
  • Basaraken Da Aka Sace A Kogi Ya Kuɓuta Bayan Shafe Kwanaki 27 A Hannun ‘Yan Bindiga 
  • Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutane 8 A Jihar Filato
  • Duk Da Cewa Wike Ba Ɗan APC Ba Ne Amma Muna Jin Daɗin Aikin sa – Tinubu