Aminiya:
2025-07-03@02:02:28 GMT

An kama ƙasurgumin ɗan bindiga yayin tantance alhazai a Abuja

Published: 18th, May 2025 GMT

Wani mutum da ake nema ruwa a jallo bisa zargin garkuwa da mutane an kama shi a sansanin alhazai da ke Abuja.

Wata majiya daga jami’an tsaro ta tabbatar wa wakilinmu cewa an kama wanda ake zargin, mai suna Yahaya Zango, yayin da ake tantance takardun maniyyatan da ke shirin tafiya Ƙasar Saudiyya domin aikin Hajjin bana.

’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa.Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027?

Rahotanni sun bayyana cewar Zango yana zaune ne a unguwar Paikon-Kore da ke cikin Ƙaramar Hukumar Gwagwalada a Babban Birnin Tarayya, Abuja.

Jami’an tsaro sun bayyana shi a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo saboda zarginsa da hannu wajen garkuwa da mutane.

Majiyar ta ce mutumin ya zo da fasfonsa tare da sauran maniyyatan Abuja, amma jami’an hukumar DSS suka gane shi kuma suka cafke shi nan take suka tafi da shi.

Wani babban jami’i daga hukumar jin daɗin alhazai, ya tabbatar da kama shi, amma ya buƙaci a sakaya sunansa.

Rahotanni sun nuna cewa an daɗe ana nemansa kafin daga bisani aka yi nasarar cafke shi.

Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan Abuja, SP Josephine Adeh, ta ce: “Ka ce DSS ce ta kama shi, amma ni kakakin rundunar ’yan sandan Abuja ce.”

DSS dai ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Kasancewar Najeriya na fama da matsalolin tsaro, hukumomi na ci gaba da ƙoƙarin magance su, duk da cewar har yanzu ana fama da barazanar hare-haren ’yan ta’adda.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Bindiga garkuwa da mutane Tantancewaz DSS

এছাড়াও পড়ুন:

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

A kakar da ta wuce, Arsenal ta karɓi Neto a aro daga Bournemouth domin taimaka wa Raya, amma yanzu ta yanke shawarar dawo da shi domin ɗaukar Kepa daga Chelsea.

Kepa ya buga wasanni 163 a Chelsea, kuma yana cikin tawagar da ta lashe kofin zakarun Turai, Europa League da kuma kofin ƙungiyoyin duniya (Club World Cup).

Haka kuma, ya shafe shekara guda a aro a Real Madrid, inda ya taimaka musu suka lashe Laliga da Champions League a kakar 2023-24.

Chelsea ta ɗauki Kepa ne a 2018 bayan kasa ɗaukar Thibaut Courtois daga Atletico Madrid da Alisson Becker wanda ya koma Liverpool.

Daga baya kuma ta gane cewa bai cancanci kuɗin da aka kashe a kansa ba, ciki har da albashin fam 190,000 da yake karɓar duk mako.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea
  • ’Yan sanda sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa a Jigawa
  • An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
  • Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu
  • Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
  • Jami’an tsaro sun tarwatsa taron kwamitin amintattun PDP
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4
  •  Wani Dan Bindiga Dadi Ya Kashe Ma’aikatan Kashe Gobara 2 A Amurka
  • Iran: An Kama Wani Dan Leken Asirin “Mosad” A Tehran A Jiya Lahadi