Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City
Published: 29th, June 2025 GMT
Tsohon tauraron ƙungiyoyin Manchester United da Real Madrid, Ruud van Nistelrooy ya ajiye aikinsa na horas da Leicester City bisa fahimtar juna.
Wannan na zuwa ne bayan da a ƙarƙashin jagorancinsa ƙungiyar ta yi wasanni 27 da ta gaza taɓuka abin a zo a gani a cikinsu, lamarin da ya kai ta ga faɗawa gasa mai daraja ta biyu a Ingila wato Championship.
Wata sanarwa da kungiyar ta fitar, ta ce an cimma matsaya tsakaninta da Van Nistelroy ne bayan tattaunawar da suka yi.
A ƙarshen watan Nuwamban da ya gabata, bayan da ta kori Steve Cooper a lokacin da suke matsayi na 16 a gasar Firimiyar bara, Liecester City ta ƙulla yarjejeniya da Van Nistelrooy, kwangilar da ba za ta ƙare ba sai a shekarar 2027.
To amma duk da sauyin da aka samu kwalliya ta gaza biyan kuɗin sabulu domin kuwa a haka suka yi ta tafiya da ƙyar.
Daga ƙarshe ma dai ƙungiyar ta sha kashi da ci 1-0 a karawar ta Liverpool a ranar 20 ga watan Afrilu, rashin nasarar da ta tabbatar da cewar ƙungiyar ta yi adabo da gasar Firimiya sai kuma wani jiƙon.
A halin yanzu dai ana sa ran tsohon Kocin Burnley da Everton, Sean Dyche ya maye gurbin da Nistelrooy ya bari.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Palasdinawa Sun Karbi Gawawwakin Shahidai 15 Daga ‘Yan Mamaya
Ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza ta sanar da karbar gawawwakin shahidai 15 a jiya Laraba a karkashin yarjejeniyar musayar fursunoni, da kungiyar agaji ta “Red Cross” ta shiga tsakani.
Sanarwar ma’aikatar kiwon lafiyar ta Palasdinu ta kuma ce, daga lokacin da aka fara musayar zuwa yanzu,adadin gawawwakin shahidan da su ka karba sun kai 345, kuma an riga an gudanar da gwaje-gwaje akan 9 daga cikinsu domin tantancewa.
Mai magana da kungiyoyin agaji Mahmud Basal ne ya tabbatar da karbar gawawwakin na shahidai da mika su ga asibitin Nasar da yake a Khan-Yunus a kudancin Gaza.
Tun da fari, ‘yan gwgawarmaya a Gaza sun mika gawar wani sojan mamaya da marecen shekaran jiya Talata.
A gefe daya kakakin kungiyar Hamas, Hazim Kassim ya ce; Mika gawar sojan mamaya yana a karkashin aiki da yarjejeniyar da aka cimmawa ne ta tsagaita wutar yaki.”
Haka nan kuma Kassim ya yi kira ga masu shiga tsakani da su yi matsin lamba ga Haramtacciyar Kasar Isra’ila akan ta dakatar da keta yarjejeniyar tsagaita wuta.”
Tun bayan tsagaita wutar yaki a Gaza dai Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta ci gaba da kai wa zirin na Gaza hare-hare da a sanadiyyarsa fiye da Falasdinawa 300 su ka yi shahada.
A nata gefen, kungiyar gwagwarmaya sun mika wa Haramtacciyar Kasar Isra’ila gawawwakin fursunoni 26 daga jumillar 28.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon Dake Takawa Makiya Birki November 27, 2025 Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa November 27, 2025 An Zabi Iran A Cikin Majalisar Zartarwa Ta Hukumar Yaki Da Makamai Masu Guba Ta Duniya CWC November 27, 2025 HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin November 27, 2025 Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta November 27, 2025 An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki November 27, 2025 Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan November 27, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza November 26, 2025 Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu. November 26, 2025 Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci