Iran ta nuna makamai masu linzami wadanda suka bude kofofin jahannama kan ‘yan sahayoniyya

A martanin da gwamnatin yahudawan sahayoniyya suka kai wa Iran, sojojin Iran da dakarun kare juyin juya halin Musulunci na kasar sun nuna karfinsu na soji a matsayin wani bangare na “Alkawarin Gaskiya na 3”, inda suka harba daruruwan makamai masu linzami na ballistic da hypersonic.

A wani bangare na wannan harin na ramuwar gayya, Iran ta kai jerin hare-hare na hadin gwiwa, wanda kaso mafi tsoka na makamai masu linzami kamar Emad, Ghadr, Fattah 1, Sejjil da Khaybar.

A halin yanzu rahotonni da hotuna daga haramtacciyar kasar Isra’ila suna kara fitowa kan yadda makamai masu linzamin Iran suka tarwatsa wurare masu muhimmanci na gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ‘yan mamaya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta dakatar da bai wa Ukraine tallafin makamai

Amurka ta dakatar da tallafin makaman da take bai wa Ukraine, tana mai bayyana damuwa kan raguwar makamanta a rumbun adana su.

Mai magana da yawun Fadar Gwamnatin Amurka, Anna Kelly a watan sanarwar da ta fitar, ta ce a halin yanzu muradun Amurka ne kan gaba ta bangaren tsaro, don haka dole ne ta dakatar da duk wani tallafin makamai da take bai wa Ukraine din.

Hamas ta karɓi tayin tsagaita wuta a Gaza Za mu ɗauki mataki kan mambobinmu da ke shirin shiga haɗakar ADC — PDP

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da Rasha ke ci gaba da fadada hare-harenta a kan kasar, yayin da aka kwashe sama da shekaru biyu ana gwabza yaki tsakanin kasashen da ke makwabtaka da juna.

Rahotanni na cewa, Ukraine za ta shiga tsaka mai wuya, musamman yadda za ta ci gaba da fuskantar Rasha ba tare da irin makaman Amurka ba,  yayin da Shugaba Vladimir Putin, ya shawarci Ukraine din da ta mika wuya.

Tuni aka shiga damuwa a wannan kasa da ke gabashin Turai, inda gwamnatin kasar ke ganin daga lokacin da aka fara samun tsaikon tallafin Amurka, Rasha za ta kara samun kwarin gwiwar kai farmaki babu kakkautawa.

A halin da ake ciki Ukraine ta shiga tsaka mai wuya, domin baya ga katse tallafin makamai, matakin da shugaba Trump ya dauka na dakatar da ayyukan Hukumar Raya Ƙasashe ta Amurka, ya shafi ayyukan jin kai a wannan kasa, sakamakon cewa tana cikin kasashen da suke karbar tallafin USAID sosai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi
  • Amurka ta dakatar da bai wa Ukraine tallafin makamai
  • Iraki Ta Kai Karar HKI Kan Amfani Da Sararin Samaniyar Kasar Don Kaiwa Iran Hare hare
  • Amurka Ta Dakatar Da Tura Makamai Zuwa Kasar Ukraine Saboda Kada A Sami Karancinsu A Gida
  • Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • Iran Ta Bawo Mayakan Huthi Fasahar Kera Makamai Masu Linzami Daga Cikin Ruwa