Aminiya:
2025-08-16@12:14:17 GMT

Za mu shige gaba idan aka dawo da tattauna shirin nukiliyar Iran — EU

Published: 2nd, July 2025 GMT

Kungiyar Tarayyar Turai EU ta bukaci a sake komawa teburin tattauna shirin nukiliyar Iran cikin gaggawa, inda take neman hadin kai a tsakanin Tehran da kuma Hukumar Kula da Makamashi ta Duniya IAEA.

Babbar jami’ar diflomasiyyar EU Kaja Kallas ta shaida wa Ministan Harkokin Kasashen Ketare na Iran, Abbas Aragchi cewar Brussels a shirye take ta shige gaba don ganin an koma teburin tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran bayan hare-haren Amurka a tashoshin makamashinsu.

HOTUNA: An yi jana’izar Dantata a Madina Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza

Bayan wata doguwar tattaunawa ta wayar tarho da jami’ar ta yi da Mista Argchi, ta wallafa a shafinta na X cewar ya kamata a koma tattaunawa kan makamashin Iran cikin gaggawa, kuma akwai bukatar hadin kai daga hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa domin cimma yarjejeniya.

Kazalika Kallas ta gargadi Tehran cewar duk wani yunkuri na janyewa daga tattaunawar ka iya dagula al’amura.

Wannan na zuwa ne bayan da Tehran ta yi watsi da sake komawa kan teburin tattaunawa da hukumar ta yi, inda Tehran ta ce tana bukatar tabbacin Amurka ba za ta sake kai mata hari ba.

A baya dai EU ta kasance mai shiga tsakani a yarjejeniyar nukiliyar Iran na 2015 da aka cimma da manyan kasashen duniya, kafin daga bisani Shugaba Donald Trump na Amurka ya yi watsi da yarjejeniya a shekarar 2018.

AFP

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Iran nukiliyar Iran

এছাড়াও পড়ুন:

An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi

Jami’an tsaro sun kuɓutar da wasu fasinjoji 10 da aka yi garkuwa da su a hanyar Itobe – zuwa Ochadamu – Anyigba a Ƙaramar hukumar Ofu a Jihar Kogi.

Fasinjojin da aka kuɓutar an yi garkuwa da su ne a ranar 11 ga watan Agusta a ƙauyen Ugbakpedo da ke kan titin, lokacin da wata mota ta yi wa fasinjojin kwanton ɓauna.

Tinubu ya bar Abuja zuwa Japan da Brazil Matsalar ƙofa ta hana fasinjoji 58 hawa jirgin Abuja zuwa Landan

Jami’an tsaron da suka haɗa da: ’yan sanda da ’yan banga da mafarautan yankin sun bayyana cewa sun afkawa dajin da ke yankin kafin ceto matafiyan.

“A ranar 13 ga watan Agusta da misalin ƙarfe 4:30 na Asubahi ne yayin wani gagarumin farmaki tare da amfani da hayaƙi mai sa hawaye, masu garkuwa da mutanen suka yi watsi da waɗanda kama suka gudu.

“An ceto dukkan mutane 10 da aka yi garkuwan da su ba tare da sun samu rauni ba, kuma tuni aka  haɗa su da iyalansu,” in ji wani rahoton tsaro kan lamarin.

Rahoton jami’an tsaro ya ƙara da cewa, ana ƙara tattara bayanan sirri da sa ido da kuma ganowa tare da yunkurin kama waɗanda ake zargin da suka tsere inda zargin masu garkuwa da mutane ne.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar (PPRO), SP William Aya ya tabbatar da ceto matafiya da aka yi garkuwa da su a ranar Juma’a a Lokoja.

Ya ce, an kuɓutar da matafiyan ne tare da haɗin gwiwa jami’an tsaro, tare da ‘yan banga da mafarauta wanda ya yi nasarar ceto waɗanda aka sace.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Takht-Ravanchi: Iran a shirye take ta ci gaba da tattaunawa kan hakkinta na nukiliya
  • Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure
  • China Tace Bata Goyon Bayan A Sake Dorawa Iran Takunkuman MDD
  • UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya
  • An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi
  • Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
  • Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin
  • Sayyid Huthi Ya Yi gargadi Yiyuwar Tarwatsewar kasashen yankin idan HKI Ta  Tabbaga Shirinta
  • Iraki Tace: Ita Yentacciyar Kasashe Ce Bayan da Amurka Ta Yi Korafi Kan Yarjeniyar tsaro da Iran
  • Ministan Harkokin Wajen Masar Ya sake Ganawa da Aragchi Da Kuma Gorossy