Muna sane da wuraren da ake yaki masu taba zuciya: Gaza, Sudan, Ukraine da sauran wurare. Rikicin baya-bayan nan tsakanin Iran da Isra’ila, wani abin tunatarwa ne ga raunin zaman lafiya musamman a yankin Gabas ta Tsakiya mai fama da tashe-tashen hankula.

 

Duk da haka, a cikin wannan tashin hankali, mun yi nasarar dakile yakin duniya na uku.

A wannan zamani na nukiliya, wannan nasara ce da ba za mu taba dauka da wasa ba. Ita ce wacce ta kamata mu kiyaye da karfin kokarinmu.

 

A cikin shekaru 80 da suka gabata, yawancin ci gaban dan’Adam shi ma yana da tasiri a MDD kai tsaye. Yi la’akari da nasarar da aka samu ta ci gaban karni, wanda kasashe mambobi 189 suka karba a cikin kasashe 2000 da kari.

 

Fiye da kungiyoyin kasa da kasa 20 ne suka ba duniya taswirar hanya daya domin daukar mataki.

 

A 2015, idan aka kwatanta da 1990, matsanancin talauci ya ragu sama da rabi. Mutuwar yara ta ragu da kusan kashi 50 cikin dari. Kuma miliyoyin yara musamman ‘yan matan da ake dannewa hakki sun shiga makaranta a karon farko.

 

Akwai wani muhimmin labarin ci gaba, wanda ba a mantawa da shi, shi ne wargaza daula. Shekaru 80 da suka gabata, mulkin mallaka ya yi shuhura a duniya. A yau, fiye da 80 da aka yi musu mulkin mallaka a fadin Asiya, Afirka, Caribbean, da Pacific sun sami ‘yancin kai kuma sun shiga MDD. Wannan canji da wannan Kungiya ta goyi baya kuma ta halalta shi ya sake fasalin tsarin duniya.

 

Shiga Tsakani domin samar da ci gaba

 

Duniya ta canza sosai tun daga 1945. A yau, kungiyar na fuskantar matsalar karancin kudi. Duk da alkawalin da aka yi na 2030 don samar da ci gaba mai dorewa, ci gaban kuma bai daidaita ba. Daidaiton jinsi ya kubuce mana. Alkawarin da muka yi na takaita hauhawar dumamar duniya da kare duniyarmu ya karanta.

 

Wadannan koma baya ba sun haifar da raguwar buri amma su ne manyan kudurorinmu. Majalisar Dinkin Duniya na nuna kimarta a lokutan rikici. Wadanda suka kafa ta sun shaida dan’Adam a matsayin mafi barna kuma ba su yanke kauna ba, saboda karfin hali. Dole ne mu zayyana wadannan nasarori.

 

Yayin da muke bikin wannan zagayowa, dole ne mu sake farfado da kiran hadin kai da aka yi daga San Francisco shekaru 80 da suka gabata.

 

Mun gina tsarin duniya farat daya, domin rushe tsarin yaki. Mun yi hakan ne da hangen nesa cikin gaggawa. Yanzu kuma, mun sami kanmu a lokacin sakamako. Hadarin yana da yawa. Haka zalika kuma karfinmu na yin aiki na da yawa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas

Ana fargabar cewa wata mata mai suna Success ta kashe wata yarinya mai shekaru bakwai, Alicia Olajumoke, a unguwar Rumueme da ke birnin Fatakwal na Jihar Ribas.

Mazauna yankin sun shaida wa Aminiya cewa matar da ake zargin tana da kusanci da dangin mahaifiyar yarinyar, wacce ita kaɗai ce a wurin iyayenta.

El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya

Bayanai sun ce ita ma matar ta caka wa kanta wuƙa a wuya bayan kashe yarinyar, kuma bayan an garzaya da duk su biyun asibiti, likitoci suka tabbatar da cewa sun riga mu gidan gaskiya.

Lamarin wanda ya faru a ranar Talata ya ɗimauta mazauna yankin, la’akari da zargin cewa matar ta kashe yarinyar ce a gidanta bayan ta je har makarantarsu ta ɗauko ta ba tare da izinin mahaifiyarta ba.

Jami’ar hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sanda a Jihar Ribas, SP Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis, inda ta ce an kai gawar yarinyar ɗakin ajiye gawa domin bai wa likitoci damar kammala bincikensu na kimiyya gabanin soma nasu binciken.

“Mun ziyarci wurin da abin ya faru, mun ɗauki hotuna, kuma an garzaya da su asibiti inda aka tabbatar da mutuwarsu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • Najeriya : Ana ci gaba da alhinin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Super Falcons za su ƙaurace wa wasannin Nijeriya saboda riƙe musu alawus
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin