Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-08-01@09:16:24 GMT

Gwamnatin Jihar Kano Ta Kebe Filin Gina Hedikwatar NWDC

Published: 14th, March 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Kano Ta Kebe Filin Gina Hedikwatar NWDC

Hukumar raya yankin arewa maso yamma NWDC ta bukaci gwamnatocin jihar Kano da su taimaka tare da hadin gwiwa da nufin cimma manufofinta.

 

 

Shugaban Hukumar Alhaji Isma’il Lawal Abdullahi Yakawada ya nemi hadin kan a lokacin da ya jagoranci mambobin hukumar a ziyarar ban girma da suka kai wa gwamnan a gidan gwamnatin Kano.

 

 

Ya ce hukumar ta NWDC na da burin tabbatar da ci gaba da bunkasar jihohin Arewa maso Yamma, tare da mai da hankali wajen magance matsalolin da suka addabi kasa kamar rashin tsaro, yunwa, fatara, da rashin abinci mai gina jiki.

 

Ya nemi goyon bayan da ake bukata da hadin gwiwar gwamnatin jihar Kano domin cimma aikin da ke gabansa.

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yabawa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu kan kafa hukumar NWDC, inda ya yaba da matakin sanya hedikwatar hukumar a Kano ba tare da la’akari da harkokin siyasa ba.

 

Gwamnan ya jaddada aniyar gwamnatin jihar Kano na tallafawa manufofin hukumar, tare da amincewa da kafa hukumar ta NWDC a kan lokaci domin tunkarar kalubalen da yankin ke fuskanta.

 

“Mun riga mun samar da filin da ya dace wanda zai yi aiki don gina ofisoshin wannan hukuma mai daraja.”

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ci gaba da cewa, yankin Arewa maso Yamma na fuskantar kalubale da suka hada da rashin tsaro, garkuwa da mutane, fashi da makami, da sauran ayyukan muggan laifuka.

 

 

” Ana sa ran kafa hukumar ta NWDC zai taimaka wajen magance wadannan al’amura, da inganta ci gaban tattalin arziki, hadin kan al’umma, da inganta rayuwar jama’a.”

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF

Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF), ta yi korafin cewa Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu ta mayar da yankin saniyar ware a kasafin ayyukan raya kasar da take yi a yankin.

Da yake jawabi yayin wani taron tattaunawa da ’yan kasa da Gidauniyar Tunawa da Ahmadu Bello ta shirya a Kaduna ranar Talata, Shugaban Kwamitin Amintattu na ACF, Alhaji Bashir Dalhatu (Wazirin Dutse), ya yi zargin cewa ana nuna wa yankin bambanci a muhimman manufofin gwamnati da kuma aiwatar da ayyukan raya kasa.

ACF ta ce hakan na faruwa ne duk da irin irin tarin gudunmawar da yankin ya ba gwamnatin mai ci a zaben 2023 da ya gabata.

DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya

Taron dai mai taken: “Nazarin alkawuran zabe: Inganta alakar gwamnati da ’yan kasa domin hadin kan kasa” ya tara gwamnoni da manyan masu rike da mukaman Gwamnatin Tarayya, ciki har da ministoci da sarakunan gargajiya da kuma kungiyoyin fararen hula.

A cewar wadanda suka shirya taron, an shirya shi ne domin karfafa fahimtar juna tsakanin mahukunta da kuma mutane a fadin arewacin Najeriya.

Sai dai wasu majiyoyi sun shaida mana cewa akwai yiwuwar Gwamnatin Tarayya ce ta hada kai da gidauniyar domin a fito da ayyukan gwamnatin a Arewa a daidai lokacin da ake ci gaba da korafin mayar da yankin saniyar ware.

Hakan, a cewar majiyoyin ba zai rasa nasaba da yadda aka ga tarin masu rike da mukamai a gwamnatin da kuma mambobin jam’iyyar APC mai Mulki suka halarci taron ba.

Daga cikin mahalarta taron dai akwai akwai wakilin Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume da Mai ba Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu da kuma Gwamnonin Kaduna (Uba Sani), Gombe (Muhammad Inuwa Yahaya) da Kwara (AbdulRahman AbdulRasaq).

Daga cikin Ministocin da suka sami halartar taron kuwa akwai na Tsaro, Badaru Abubakar, da Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle da na Yada Labarai, Mohammed Idris, da Karamin Ministan Ayyuka, Muhammed Bello Goronyo da Karamin Ministan Gidaje, Yusuf Abdullahi Ata da kuma Karamar Ministar Abuja, Mariya Mahmud Bunkure.

Sauran sun hada da Babban Hafsan Tsaro na Najeriya, Christopher Musa da Babban Hafsan Sojojin Sama, Hassan Abubakar da kuma shugabar hukumar kula da shige da fice ta Najeriya, Kemi Nandap.

Akwai kuma tsofaffin Gwamnoni irin su Ramalan Yero (Kaduna), Aliyu Sjinkafi (Zamfara), Ibrahim Shekarau (Kano) da Mu’azu Babangida Aliyu (Neja) da dai sauransu.

Sai dai ko kafin taron na ranar Talata, ko a makon da ya gabata sai da tsohon Gwamnan Kano kuma dan takarar Shugaban Kas ana jam’iyyar NNPP. Azaben 2023, Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi irin wannan zargin cewa gwamnatin Tinubu na fifita kudanci a kan arewaci a fannin ayyukan raya kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa
  • Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi