Leadership News Hausa:
2025-08-12@17:32:12 GMT

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Published: 28th, June 2025 GMT

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Kasashen Kenya da Tanzaniya da kuma Uganda sun gabatar da kasafin kudin da ya mayar hankali kan zabuka da tattalin arzikin kasashen.

Galibi kasafin kudin kasahen Afirka kan mayar da hankali wajen cimmma muradunsu na tattalin arziki da ci gaba.

Kasafin kudin kasashen Afirka na 2025 na kunshe da muradun ci gaba da bunkasar abubuwan more rayuwa da kuma ingantuwar al’amuran yau da kullum a kasashen.

Kunshin kasafin kudin kasashen Afirka na 2025 ya ware gagarumin kaso a fannin inganta abubuwan more rayuwa da ayyukan kyautata rayuwar al’umma da kuma bunkasa tattalin arzikin kasashen.

Kowace shekara kasashen Afirka na ware makudan kudade a kasafin kudadensu.

A wannan makala mun zakulo kuku kasashen Afirka 10 da suka fi girman kasafin kudi, kuma mun yi kiyasin da Dala domin samun saukin lissafi.

Afirka ta Kudu – (Dala biliyan 141.4)

Kasar Afirka ta Kudu ce kan gaba wajen ware makudan kudade a kasafin kudi a Afirka a 2025.

A wannan shekara kasar ta ware Dala biliyan 141.4 a matsayin kasafin kudiinta.

Kasafin kudin ya fifita fannin abubuwan more rayuwa da ayyukan bunkasa rauyuwar jama’a da ci gaban tattalin arziki.

Algeria – (Dala biliyan 126)

Kasar Algeria ce ke matsayi na biyu a yawan kasafin kudi a nahiyar Afirka a 2025. Kasar – wadda ke arewacin Afirka – ta ware Dala biliyan 126 a kasafin kudinta, inda tafifita fannnonin makamashi da tsaro.

Masar – (Dala biliyan 91)

Masar ce ta uku cikin jerin, mai adadin kudi har Dala biliyan 91, inda ta ware kaso mai yawa zuwa fannonin ilimi da lafiya da ayyukan da za su amfani jama’a.

Morocco – (Dala biliyan 73)

Kasar Morocco – da ita ma ke yankin arewacin Afirka ta kasance a mataki na hudu.

Morocco ta ware Dala biliyan 73 a kasafin kudinta na shekarar 2025.

Angola – (Dala biliyan 37.847)

Angola – arzikin man fetur – ce a matsayi na biyar cikin jerin kasashen Afirka da suka fi karfin kasafin kudi.

Kasar – wadda ke yankin kudancin Afirka – ware Dala biliyan 37.847 domin kasafin kudinta na shekarar da muke ciki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ware Dala biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

“Baya ga alaƙa da Ruwa, ƙasashen da ke Afirka ta Gabas da kuma waɗanda ke a Afrika ta Tsakiya, da suke yi musharaka da irin ƙalubalensu da kuma sauran damarmakinsu, dole ne mu zage mu amfana da tattalin arzikin da ake da shin a Tekuna, musamman ta hanyar haɗa kanmu da kuma yin haɗaka, wanda idan ba a yi hakan ba, tamkar muna kawai yaudarar kawunan mu ne,” Ɗantso ya ce.

A cewar Shugaban na Hukumar NPA, alƙaluman da ake da su, sune za su bamu damar, ci gaba da ɗaukar matakan da suka kamata, na wajen ci gaba da bai wa Tashoshin Jiragen Ruwa na Afrika, kulawar da ta dace.

Kazalika, Shugaban ya kuma jinkinawa shugaban ƙasa Bola Tinubu, kan ƙirƙiro da Ma’aikatar Kula da Tattalin Arziki na Teku, inda ya sanar da cewa, hakan ya samar wa da Hukumar ta NPA sauƙi wajen samar da inagantattun sauye-sauyen a fannin na tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar.

“Gwamnatin mai girma Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa ƙirƙiro da Ma’aikatar Kula da Tattalin Arziki na Teku, hakan ya samar wa da Hukumar mu ta NPA samun sauƙin samar da ingantattun sauye-sauye, a fannin na tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwan Ƙasar nan, inda kuma ta hanyar Ma’aikatar, a ƙara samar da ɗimbin masu zuba hannun jari a fannin tare da kuma amfana da basira ƙwararrun da ke a ƙungiyar ta PMAWCA,” Inji Shugaban.

Ɗantsoho ya ci gaba da cewa, ƙwararrun da ke kula da kafar sadarwar, suma suna ci gaba da taimaka wa wajen ƙara samar da horo domin a amfana da damarmakin da ke a Tashoshin na Jiragen Ruwan, musamman ta hanyar amfani da tsarukan PCS NSW.

Shugaban na Hukumar ta NPA ya ƙara da cewa, dole ne, a ci gaba da yin ƙoƙarin da ake gudanarwa kafaɗa da kafaɗa, ta hanyar haɗa kai da sauran ‘ya’yan ƙungiyar ta PMAWCA.

“Manufofin yarjejeniyar kasuwanci marar shinge ta Afrika wato AfCFTA, sun haɗa da kawar da haraji da kuma duk wani harajin da ke sanya wa, na gudanar da hada-hadar kasuwanci, wanda hakan zai kuma ƙara samar da sauran damarmaki a fannnin da kuma ƙara samun ɗaukaka fannin,” Inji Ɗantsoho.

Ɗantsoho ya ƙara da cewa, a taron da Dakaratocin na ƙungiyar ta PMAWCA suka gudanar, sun yi nazari kan samakon ayyukan da ƙungiyar ta gudanar shekarar 2024 tare da kuma auna shawarwarin da mahalarta taron suka bayar, a lokcin taron, inda suke tsara matakan da za su ɗauka nag aba, domin ƙungiyar, ta ƙara samun ci gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila
  • Majalisar Kano Ta Karbi Kudirin Karamin Kasafin Kudi Na Shekarar 2025
  • Mafi yawan Kasashen Duniya Sun Amince Da Samarda Kasar Falasdinu
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Karɓi Ƙarin Kasafin Kuɗi Na 2025
  • Gwamna Bago Ya Kaddamar da Katafaren Kamfanin sarrafa Man Kade A Afirka.
  • Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
  • Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
  • Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
  • Iran Ta Yi Maraba Da Sulhuntawa Tsakanin Armenia Da Azerbaijan
  • Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika