Aminiya:
2025-08-17@11:12:41 GMT

2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC

Published: 2nd, July 2025 GMT

Jagoran sabuwar jam’iyyar ADC, Ralph Nwosu, ya bayyana cewa tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, zai jagorance su wajen karɓar mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

Jam’iyyar haɗakar, wacce ta ƙunshi fitattun ’yan siyasa, ta naɗa David Mark a matsayin Shugaba, tare da tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, a matsayin Sakatare.

’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba

A wajen babban taron da ta gudanar a cibiyar Yar’Adua da ke Abuja, Nwosu ya ce: “Mun sauka daga muƙamanmu domin mu bai wa David Mark dama ya jagoranci wannan tafiya zuwa fadar shugaban ƙasa.”

Ya yaba wa Aregbesola, wanda ya taɓa kasancewa abokin siyasar Tinubu, inda ya ce mutum ne mai aiki tuƙuru da kishin ƙasa.

Nwosu ya ƙara da cewa: “’Yan Najeriya sun gaji. Sun ƙosa da sauyi. Wannan haɗaka da muke yi na da matuƙar muhimmanci.

“Ina goyon bayansa sosai, kuma ba zan huta ba har sai mun isa fadar shugaban ƙasa, mun rera taken ƙasa a can. Najeriya na cikin tsaka mai wuya.

“Rayuka na salwanta kullum. Shugabanninmu na gaba su fitar da Najeriya daga wannan halin, su kai ta ga ci gaba. Za mu iya!”

Ya kuma gargaɗi masu sukar wannan haɗakar da cewa ba ’yan jam’iyyar ADC ba ne.

“Babu buƙatar yin nadama a kan abin da muka yi yau. Wannan tafiya ce mai wahala, dole mu kasance a shirye.”

Daga cikin fitattun mutane da suka halarci taron har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar; ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi.

Sauran sun haɗa da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai; tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi; da tsohon Gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, da sauransu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: David Mark Haɗaka Zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara

“Na zo Banga domin jajanta muku bisa wannan mummunan hari. Lokacin da abin ya faru bana nan, sai na umarci mataimakina ya jagoranci tawaga ta musamman domin yi muku ta’aziyya.

“Na dawo Gusau jiya, kuma abu na farko da na fifita yau shi ne zuwa nan da kaina. Gwamnati za ta ƙara ƙoƙari wajen yaƙar ‘yan bindiga,” in ji shi.

Gwamnan ya yi addu’ar Allah Ya ɗauki matakaki a kan waɗanda suka aikata wannan kisan gilla, sannan ya roƙi jama’a da su ci gaba da yin addu’a domin kawo ƙarshen duk wata ɓarna a Zamfara.

Sarkin Kauran Namoda, Dokta Sunusi Ahmad Rashad, wanda ya raka gwamnan, ya yaba masa bisa saurin ɗaukar mataki bayan faruwar lamarin.

“Wannan ziyara tana da matuƙar muhimmanci ga mutanen da abin ya shafa. Muna godiya, kuma Allah Ya ci gaba da maka jagoranci,” in ji shi.

Gwamna Lawal ya kuma yi alƙawarin inganta ayyukan more rayuwa a yankunan, kamar hanyoyi, wutar lantarki, ruwan sha, da sauransu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APC ta lashe zaɓen cike gurbi na Ghari/Tsanyawa a Kano
  • HOTUNA: Yadda zaɓen cike gurbi ke gudana a sassan Najeriya
  • An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
  • An kafa dokar hana zance tsakanin saurayi da budurwa a Kano
  • An Biya Falcons Duk Kuɗin Alawus, Kyautar $100,000 Da Gidaje Ga Super Falcons
  • ASCSN Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Nada Muhammad Dagaceri Shugaban Ma’aikata
  • Kotun kasar Kanada ta ayyana APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci
  • NAJERIYA A YAU: Halin ƙuncin da ’yan fansho ke ciki a Najeriya
  • Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara
  • Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse