Aminiya:
2025-10-13@18:07:14 GMT

2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC

Published: 2nd, July 2025 GMT

Jagoran sabuwar jam’iyyar ADC, Ralph Nwosu, ya bayyana cewa tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, zai jagorance su wajen karɓar mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

Jam’iyyar haɗakar, wacce ta ƙunshi fitattun ’yan siyasa, ta naɗa David Mark a matsayin Shugaba, tare da tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, a matsayin Sakatare.

’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba

A wajen babban taron da ta gudanar a cibiyar Yar’Adua da ke Abuja, Nwosu ya ce: “Mun sauka daga muƙamanmu domin mu bai wa David Mark dama ya jagoranci wannan tafiya zuwa fadar shugaban ƙasa.”

Ya yaba wa Aregbesola, wanda ya taɓa kasancewa abokin siyasar Tinubu, inda ya ce mutum ne mai aiki tuƙuru da kishin ƙasa.

Nwosu ya ƙara da cewa: “’Yan Najeriya sun gaji. Sun ƙosa da sauyi. Wannan haɗaka da muke yi na da matuƙar muhimmanci.

“Ina goyon bayansa sosai, kuma ba zan huta ba har sai mun isa fadar shugaban ƙasa, mun rera taken ƙasa a can. Najeriya na cikin tsaka mai wuya.

“Rayuka na salwanta kullum. Shugabanninmu na gaba su fitar da Najeriya daga wannan halin, su kai ta ga ci gaba. Za mu iya!”

Ya kuma gargaɗi masu sukar wannan haɗakar da cewa ba ’yan jam’iyyar ADC ba ne.

“Babu buƙatar yin nadama a kan abin da muka yi yau. Wannan tafiya ce mai wahala, dole mu kasance a shirye.”

Daga cikin fitattun mutane da suka halarci taron har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar; ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi.

Sauran sun haɗa da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai; tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi; da tsohon Gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, da sauransu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: David Mark Haɗaka Zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako

An kammala kada ƙuri’a da yammacin Lahadi a zaɓen shugaban ƙasa na Kamaru, inda shugaban ƙasa mai shekaru 92, Paul Biya — wanda shi ne tsohon shugaban ƙasa mafi tsufa a duniya — yake neman wa’adi na takwas a mulki.

Biya, wanda ya shafe shekaru 43 yana mulkin ƙasar, ya fafata da ’yan takara 11, ciki har da tsoffin muƙarrabansa.

Ɗaya daga cikinsu shi ne Issa Tchiroma Bakary, tsohon ministan ma’aikata wanda ya yi murabus daga gwamnati a watan Yuni bayan fiye da shekaru 20 yana aiki tare da Biya.

Bakary, mai shekaru 79, ya zama babban abokin hamayyar Biya bayan Kotun Tsarin Mulki ta ƙi amincewa da takarar fitaccen ɗan adawa Maurice Kamto — matakin da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam ciki har da Human Rights Watch suke cewa ya rage sahihancin tsarin zaɓen.

Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya Matasa da dogon mulki

Kamaru na da masu kaɗa ƙuri’a kusan miliyan takwas, yawansu matasa da ba su taɓa sanin wani shugaban ƙasa ba sai Biya, tun da ya hau mulki a 1982.

A cikin shekaru 20 da suka gabata, Biya yakan lashe zaɓe da sama da kashi 70 na ƙuri’u.

Bayan ya jefa ƙuri’arsa a kusa da fadar gwamnati a Yaounde, Biya ya ce wa manema labarai: “Ba a san komai ba tukuna. Mu jira mu ga wanda aka zaɓa.”

Wani jami’in hukumar zaɓe ta ƙasa, Jean-Alain Andzongo, ya shaida wa AFP cewa an gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da tsari a babban birnin.

Mai sharhi kan harkokin siyasa, Stephane Akoa, ya ce duk da cewa jam’iyyar mai mulki na da damar ganin ta sami nasara, wannan yaƙin neman ya kasance “mai ɗan ɗumi fiye da yadda aka saba,” yana nuna yiwuwar “samun wasu abubuwan mamaki.”

’Yan takara da yaƙin neman zaɓe

Biya bai yi fitowa sosai ba a lokacin yaƙin neman zaɓe, inda ya bayyana sau ɗaya kacal a wani babban gangami a Maroua, a yankin Arewa Mai Nisa — inda akwai masu kaɗa ƙuri’a miliyan 1.2.

Sai dai wannan yankin da aka daɗe ana ɗauka matsayin ginshikin goyon bayansa, yanzu wasu tsoffin abokansa ne ke takara da shi daga yankin.

’Yan adawa sun gudanar da gangami a sassa daban-daban na ƙasar, suna alkawarin kawo sauyi ga al’ummar Kamaru.

A yayin da Biya ya tara ’yan ɗaruruwan mutane kaɗan a gangaminsa, Bakary kuwa ya samu tarbar dubban magoya baya a yankin da ya fito, suna ɗaga tutoci masu taken “Tchiroma Mai Ceto.”

Tattalin arziki da ƙorafin jama’a

Duk da albarkatun ƙasar – musamman noma da ma’adinai – Kamaru na ci gaba da fama da talauci da rashin aikin yi.

Bisa ga rahoton Bankin Duniya (2024), kusan kashi 40% na ‘yan ƙasar na rayuwa ƙasa da layin talauci, yayin da rashin aikin yi ya kai kashi 35% a manyan birane.

Jama’a na ci gaba da koka kan tsadar rayuwa, ƙarancin ruwan sha mai tsafta, rashin ingantaccen kiwon lafiya da kuma matsalolin ilimi.

Matasa da neman sauyi

Akoa ya bayyana cewa matasan Kamaru na ƙaunar ganin sauyi, amma har yanzu ba su kai matakin yin zanga-zanga kamar yadda ake gani a wasu ƙasashe na Afirka da Asiya ba.

Ya ce: “Yawancin matasa sun nuna niyyar kaɗa ƙuri’a. Wannan alama ce mai kyau, amma ba ta kai matakin tayar da gagarumin yunƙuri irin na Madagascar ko Tunisia ba.”

Sauran bayanai da sakamakon zaɓe

Gwamnatin Kamaru ta bai wa masu lura da zaɓe kusan 55,000 — ciki har da wakilan Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) — damar sa ido kan zaɓen.

Kotun Tsarin Mulki na da wa’adin Oktoba 26 don fitar da sakamakon ƙarshe.

Sai dai wasu kafafen sada zumunta sun sanar da shirinsu na tattara sakamako da kansu — abin da gwamnati ta soki, tana zargin suna ƙoƙarin karkatar da ra’ayoyin jama’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta
  • Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole