Aminiya:
2025-07-03@03:13:21 GMT

2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC

Published: 2nd, July 2025 GMT

Jagoran sabuwar jam’iyyar ADC, Ralph Nwosu, ya bayyana cewa tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, zai jagorance su wajen karɓar mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

Jam’iyyar haɗakar, wacce ta ƙunshi fitattun ’yan siyasa, ta naɗa David Mark a matsayin Shugaba, tare da tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, a matsayin Sakatare.

’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba

A wajen babban taron da ta gudanar a cibiyar Yar’Adua da ke Abuja, Nwosu ya ce: “Mun sauka daga muƙamanmu domin mu bai wa David Mark dama ya jagoranci wannan tafiya zuwa fadar shugaban ƙasa.”

Ya yaba wa Aregbesola, wanda ya taɓa kasancewa abokin siyasar Tinubu, inda ya ce mutum ne mai aiki tuƙuru da kishin ƙasa.

Nwosu ya ƙara da cewa: “’Yan Najeriya sun gaji. Sun ƙosa da sauyi. Wannan haɗaka da muke yi na da matuƙar muhimmanci.

“Ina goyon bayansa sosai, kuma ba zan huta ba har sai mun isa fadar shugaban ƙasa, mun rera taken ƙasa a can. Najeriya na cikin tsaka mai wuya.

“Rayuka na salwanta kullum. Shugabanninmu na gaba su fitar da Najeriya daga wannan halin, su kai ta ga ci gaba. Za mu iya!”

Ya kuma gargaɗi masu sukar wannan haɗakar da cewa ba ’yan jam’iyyar ADC ba ne.

“Babu buƙatar yin nadama a kan abin da muka yi yau. Wannan tafiya ce mai wahala, dole mu kasance a shirye.”

Daga cikin fitattun mutane da suka halarci taron har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar; ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi.

Sauran sun haɗa da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai; tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi; da tsohon Gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, da sauransu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: David Mark Haɗaka Zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

APC ta sa ranar taron Majalisar Zartarwa bayan murabus ɗin Ganduje

Jam’iyyar APC mai mulki a Nijeriya ta tsayar da 24 ga watan Yulin bana a matsayin ranar da za ta gudanar da taronta na Majalisar Zartarwa.

Mataimakin Sakataren jam’iyyar, Barista Fetus Fuanter ne ya tabbatar wa manema labarai hakan a yau Litinin a Abuja.

Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe Jami’an tsaro sun hana taron kwamitin amintattun PDP

Fuanter ya ce kusoshin jam’iyyar za su gana kafin gudanar da taron Majalisar Zartarwar.

Taron da za a gudanar shi ne na biyu ta fuskar girma a cikin jerin tarukan da jam’iyya ke zaman yanke shawara da daukar wasu muhimman matakai bayan babban taronta na kasa.

Wannan dai na zuwa ne yayin da ake ci gaba cece-kuce tun bayan murabus ɗin shugaban jam’iyyar na ƙasa ya yi a makon jiya.

A makon da ya gabata ne shugaban jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar, Abdullahi Ganduje, ya ajiye mulki a wani abu da masana ke cewa na da alaƙa da lisaafin da manyan ’yan siyasar ke yi gabanin Zaɓen 2027.

APC ta ce tuni Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarci Ali Bukar Dalori ya maye gurbin Ganduje a matsayin shugaba na riƙo kafin kwamatin zaɓaɓɓu su gana game da batun.

Jami’in yaɗa labarai na APC, Bala Ibrahim, ya bayyana cewa babban dalilin da Ganduje ya bayar game da murabus ɗin nasa shi ne batun ƙoshin lafiyarsa.

Sai dai wata majiya daga fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa Ganduje ya ajiye muƙamin ne bayan da fadar shugaban ta umarce shi da yin hakan.

Da ma tun lokacin aka bai wa Ganduje shugabancin jam’iyyar wasu ‘yan jam’iyyar, musamman daga yankin Arewa maso Gabas, suka riƙa gunaguni cewa su ya kamata a bai wa.

Zuwa yanzu babu tabbas game da wanda fadar shugaban ke son ya karɓi shugabancin jam’iyyar.

Daga cikin waɗanda ake raɗe-raɗin za su maye gurbin Ganduje akwai tsohon Gwamnan Nasarawa, Umar Tanko Al-Makura da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
  • Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
  • David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu
  • David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
  • Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu
  • An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
  • Uwargidar Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma
  • APC ta sa ranar taron Majalisar Zartarwa bayan murabus ɗin Ganduje
  • Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki