Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Published: 29th, June 2025 GMT
Shugaban majalisar dokokin jama’ar kasar Mexico Sergio Carlos Gutiérrez, ya bayyana yayin da wakilin babban gidan rediyo da telebijin na kasar Sin wato CMG ya zanta da shi a kwanakin baya cewa, tunanin raya al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama da shugaba Xi Jinping ya gabatar ya burge shi matuka.
Ya ce, an gabatar da tunanin don tattauna yadda sassan kasa da kasa za su zauna tare, da taimakawa juna, da amincewa da bambance-bambance a fannonin tattalin arziki, da yawan mutane, da yankunan kasa a tsakanin kasashen duniya, da sa kaimi ga maida bambance-bambance su zama hanyar dinkewa da juna, da kuma samar da kyakkyawan yanayin zaman rayuwar al’ummun kasa da kasa. Kana yana fatan jama’ar kasashen duniya ciki har da ta Sin da ta Mexico, za su ji dadin zaman rayuwa mai inganci.
Ban da wannan kuma, Gutiérrez ya yi nuni da cewa, Sin da kasashen Latin Amurka sun taimakawa juna, da more fasahohin samun ci gaban juna, da sa kaimi ga samun zaman rayuwar jama’a mai inganci, kana bangarorin biyu sun yi kokarin samar da yanayin zaman rayuwa mai tsaro, da inganci ga jama’arsu.
Ya ce, bisa yanayin da ake ciki a duniya, zurfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, zai jagoranci Sin da kasashen Latin Amurka, ga bin hanyar samar da zaman rayuwa mai inganci ga al’umma. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji
Daga ƙarshe dai Shugaban Kasa Bola Tinubu ya sa hannu kan sababbin dokokin haraji guda hudu da a baya suka jawo cece-kuce da zazzafar muhawara a faɗin Najeriya.
An dai sanya hannun ne a fadar shugaban kasa ta Aso Rock da ke Abuja ranar Alhamis, inda shugaban ya ce dokokin za su bunkasa harkokin hada-hadar kudade da tattara haraji a kasar.
NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya? Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniyaA kwanan nan ne dai Majalisar Dokoki ta Ƙasa ta amince da kudurorin su zama doka bayan tafka zazzafar muhawara a zaurukan majalisun guda biyu.
Daga cikin waɗanda suka halarci bikin saka hannun akwai Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajuddeen Abbas da shugabannin masu rinjaye na majalisun biyu da kuma shugabannin kwamitocin kudi na majalisun.
A ranar Laraba ce dai mai magana da yawun shugaba Tinubu, Bayo Onanuga, ya sanar da cewa da zarar sun fara aiki, kudurorin za su bunkasa hanyoyin tattara kudaden shiga a kasar.
A cewarsa, ana sa ran dokokin za su kuma karan yawan kudaden harajin da Najeriya ke samu sannan sau bunkasa harkokin kasuwanci su kuma haɓaka harkokin zuba jari daga ’yan kasuwar gida da na ƙetare.
Sai dai Hukumar Tattara Haraji ta Kasa (FIRS) ta ce dokokin ba za su fara aiki ba sai a watan Janairun 2026.
A baya dai saɗarorin dokokin da suka fi yamutsa hazo su ne na batun rarraba harajin kuɗaɗen sayen kaya na VAT da yadda za a raba shi.
Sai dai majalisar dattawa da ta wakilai ta gyara saɗarorin kafin ta amince da su tare da samun amincewar akasarin ’yan majalisar.