Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
Published: 29th, June 2025 GMT
Rivers Angels ta lashe gasar cin Kofin Shugaban ƙasa na shekarar 2025 bayan ta doke Nasarawa Amazons da ci 4-2 a bugun fenareti bayan da suka tashi 2-2 a filin wasa na Mobolaji Johnson dake birnin Legas, wannan ne karo na goma da ɓangaren Tosan Blackson ke lashe kofin.
Nasarawa Amazons ce ta jagoranci wasan a farko da ci 2-0 waɗanda Olusola Shobowale ta ci, Olusola ta zura ƙwallon farko a minti na 7 da fara wasan sai kuma ta zura ta biyu a minti na 10, bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ne Rivers ta zage damtse, wanda ya kai ta ga farke duka ƙwallaye biyu a cikin mintuna 5 kacal.
Taiwo Ajibade ce ta ci wa Rivers duka kwallayenta biyu a cikin mintuna 5 da dawowa daga hutun rabin lokaci, hakan ya sa wasan ya kare da ci 2-2 wanda kuma ya sa aka tafi zuwa bugun daga kai sai mai tsaron raga domin fitar da zakaran wasan, kugiyar ta Port Harcourt ya yi nasara a bugun daga kai sai mai tsaron gida bayan ta jefa kwallo 4 yayinda Amazons suka jefa kwallaye 2.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Ƙwallon Ƙafa
এছাড়াও পড়ুন:
Za a tono gawar tsohon Gwamna Alao-Akala domin gwajin jinin ’ya’yansa
Ana neman tono gawar tsohon Gwamnan Jihar Oyo, marigayi Otunba Christopher Adebayo Alao-Akala, domin yin gwajin jini (DNA) da nufin tantance halastattun ’ya’yansa da za su ci gadon dukiyar da ya bari.
Batun tono gawar ta kunno kai ne bayan taƙaddama ta yi tsami a tsakanin ’ya’yan tsohon gwamnan a kan rabon gadonsa.
Babbar ’yar marigayin mai suna Uwargida Oluwatoyin Alao-Aderinto ce ta shigar da ƙara a gaban Mai Shari’a Taiwo na Babbar Kotun Jihar Oyo ta hannun lauyanta, Oladipo Olasope (SAN), inda ta roƙi kotun ta bayar da umarnin tono gawar mahaifin nasu daga kabarinsa domin yin gwajin ƙwayar halittarsa ga wasu mutane bakwai da ke iƙirarin cewa su ne halastattun ’ya’yan marigayin.
Uwargida Aderinto ta shigar da ƙarar ne bayan abin da ta kira barazanar da ’yan uwanta ke yi na neman cire sunanta daga cikin jerin halastattun ’ya’yan marigayin da za su gaje shi.
Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a NejaA takardar ƙarar, ta bayyana cewa ɗaukar matakin tono gawar mahaifin nasu da yin gwajin jini ga ’yan uwan nata su bakwai, har da ita kanta, shi ne zai taimaka wajen tantance ainihin halastattun ’ya’yan
marigayin da suka cancanci cin gadon ɗimbin dukiyar da ya bari a ciki da wajen Nijeriya.
Tsohon Gwamna Otunba Adebayo-Alao Akala ya mutu ne cikin watan Janairu na shekarar 2022, inda aka binne shi a cikin watan Oktoban shekarar a wani ƙasaitaccen kabari da aka gina a harabar gidansa da ke mahaifarsa a garin Ogbomosho da ke jihar.
Dukiyoyin da tsohon gwamnan ya mutu ya bari da ’ya’yan nasa suke jayayya a kai, waɗanda Lauya Oladipo ya gabatar gaban kotun, sun haɗa da rukunin gidajen alfarma a biranen Ibadan da Legas da Abuja da kuma ƙasashen Amurka da Birtaniya da wani katafaren otel a ƙasar Ghana.
Sauran sun haɗa da motocin alfarma da maƙudan kuɗaɗe a bankuna daban-daban a Nijeriya da ƙasashen Amurka da Birtaniya.
Tushen rikicin rabon gadon Alao-AkalaAn fara wannan taƙaddama a tsakanin ’ya’yan tsohon gwamnan ne bayan da aka binne gawarsa a watan Oktoba na shekarar 2022.
Rikicin ya samo asali ne bayan mutum biyu daga cikin ’ya’yannsa masu suna Kemi Alao-Akala da Olamide Alabi suka samu izinin daga magatakardan kotun rabon gado na Jihar Oyo, ba tare da sani ko amincewar Uwargida Oluwatoyin Alao-Aderinto ba, a matsayinta na babbar ’ya ga marigayin.
Ta yi zargin cewa ’yan uwan nata sun kitsa lamarin ne da gangan ta bayan fage, kuma abin da suka yi ya saɓa wa dokokin rabon gado na Nijeriya. Don haka ta zargi ’yan uwan nata da neman yin kwanciyar magirbi a kan dukiyar da mahaifinsu ya bari.
A watan Agustan2023, Lauya Oladipo Olasope (SAN) ya yi zargi a cikin wata wasiƙa cewa, ƙoƙarin cire sunan Uwargida Oluwatoyin AlaoAderinto, a matsayinta na babbar ’yar Marigayi Adebayo Alao-Akala daga cikin jerin ’ya’yansa zai iya haifar da babbar ɓaraka da rabuwar kawunan wannan babban gida. Saboda haka ya nemi kotun ta hanzarta ɗaukar matakin biyan buƙatun wadda yake karewa, na tono gawar marigayin domin a kawo ƙarshen matsalar ɗungurungum.