Aminiya:
2025-08-17@06:08:21 GMT

’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe

Published: 2nd, July 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta kama wani mutum, mai shekaru 35 daga ƙauyen Kunji da ke Kwadon, bisa zargin mallakar jabun kuɗi.

Kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya ce an kama Kawu ne a ranar 28 ga watan Yuni, 2025, a ofishin ’yan sanda na Lawanti, sannan aka kai shi ofishin Amada domin ci gaba da bincike.

Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba

Ya ce an samu dalar Amurka 1,000 da ake zargin na bogi ne (kimanin Naira miliyan 1.5), da kuma Naira 10,000 a cikin kayansa.

A yayin bincike, Kawu ya amsa cewa kuɗin na wani mutum ne.

’Yan sanda sun ce suna ci gaba da bincike domin gano wanda ya ba shi kuɗin.

Rundunar ta kuma ce za ta ci gaba da yaƙar masu ta’ammali da jabun kuɗi tare da tabbatar da cewa za ta sanar da jama’a yadda binciken ke tafiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda zargi

এছাড়াও পড়ুন:

UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya

“Sama da yara miliyan 10.1 ne ba su kai makaranta, kashi 70 masu zuwa makarantar kuma ba su da dabarun koyo, kuma fiye da kashi 60 na malaman firamare na gwamnati ba su da ilimin dijital,” in ji ta

Da take yaba wa gwamnatin Koriya ta Arewa bisa tallafin da ta samu ta hannun hukumar raya kasashe ta KOICA, Garba ta ce wannan hadin gwiwa ya taimaka wa kasar wajen sake tunanin koyo, tare da dakile rarrabuwar kawuna, da bai wa makarantu da malamai kwarin gwiwa domin samar da sauyi mai dorewa.

Mataimakin Babban Sakatare na UBEC (Technical), Mista Razak Akinyemi Olajuwon, ya bayyana cewa, wannan shiri ya kara wa malamai kwarin gwiwar yin amfani da su da bunkasa abubuwan da ke cikin ICT da inganta samun nagartattun abubuwan koyarwa da fasahar sadarwa a cikin ajujuwa.

Manajan ofishin KOICA na Nijeriya Dabid Nkwa, ya ce a cikin shekaru biyar da suka gabata aikin ya inganta ilimi a Nijeriya, musamman sakamakon koyo a matakin farko na ilimi.

NELFUND Ta Raba Bashin Naira Biliyan 86.3 Ga Dalibai 450,000

susun Ba Da Lamuni Na Ilimi na Nijeriya ya sanar da cewa ya zuwa yanzu adadin dalibai 449,039 ne suka ci gajiyar shirin bayar da lamuni na dalibai tun bayan kaddamar da shirin a ranar 24 ga Mayu, 2024.

Dangane da sabon rahoton halin yau da kullun da aka fitar a ranar Litinin, 11 ga Agusta, 2025, shirin ya fitar da jimillar Naira biliyan 86,347,458,384 a ranar 6 ga Agusta, 2025.

Ta ce kudaden sun hada da Naira 47,629,338,384 da aka biya kai tsaye ga cibiyoyi 218 a matsayin kudin karatu da kuma Naira 38,718,120,000 da aka bai wa dalibai a matsayin alawus-alawus.

Rahoton ya kara da bayyana cewa dalibai 731,140 ne suka yi rajista a dandalin rancen, inda 720,732 suka samu nasarar samun lamuni, wanda ke wakiltar kashi 98 na nasarar aikace-aikacen.

Bayanai daga dashboard sun nuna karuwar yau da kullun na 933 a cikin adadin masu yin rajista da kuma karin masu nema 1,094.

NELFUND ta lura cewa “shirin yana ba da Ajandar Renew Hope na Shugaba Bola Tinubu na karfafa kowane dalibin Nijeriya ta hanyar samun tallafin ilimi.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama matashin da ya yi garkuwa da kansa a Ondo
  • An kama ’yan daba 288 yayin zaɓen cike gurbi a Kano
  • Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
  • UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya
  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hanci Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • ‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.
  • An kama Mai Unguwa kan yi wa yarinya fyaɗe a Gombe
  • ‘Yan Majalisa Na Ba Da Cin Hancin Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Iya Gabatar Da Ƙudiri – Kamfani.
  • An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun
  • ’Yan sanda sun kama matashi kan zargin aikata fashi a Gombe