Sai bayan Magariba za a yi wa Dantata jana’iza a Madina
Published: 1st, July 2025 GMT
Bayanai daga makusantan fitaccen attajirin nan da ya riga mu gidan gaskiya, Alhaji Aminu Ɗantata sun nuna cewa an ɗage jana’izarsa da aka shirya gudanarwa bayan sallar La’asar a ranar Talata.
Yanzu an mayar da jana’izar zuwa bayan Magariba a haramin birnin Madina.
Kotu za ta duba yiwuwar ba da belin Tukur Mamu a ranar 22 ga watan Yuli Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautuA wata zantawa da ya yi da BBC, Mustapha Junaid, mataimaki na musamman ga marigayin ya bayyana cewa tuni gawar Alhaji Aminu ta isa birnin na Madina.
“Alhamdu lilLah an ɗauki marigayi Alhaji Aminu Ɗantata daga filin jirgi na Madina kuma yanzu haka za a je Shakzura inda a nan ne za a ƙarasa shirya shi kafin daga bisani a kai shi haramin Madina domin gudanar da sallah kamar yadda hukumomin Saudiyya suka amince,” in ji Mustapha Junaid.
Wannan dai shi ne karo na biyu da ake sauya lokacin jana’izar mamacin wanda da farko aka ruwaito cewa za a gudanar a ranar Litinin kamar yadda Ministan Labarai, Mohammed Idris ya tabbatar.
A karon na farko dai, Ministan ya ce an ɗage jana’izar sakamakon rashin isar gawar marigayin a kan lokaci zuwa birnin Madina.
A cewarsa, “akwai ƙa’idoji da Gwamnatin Saudiyya ta shimfiɗa kan yadda za a shigar da gawa domin yi mata jana’iza a ƙasar.
“Saboda haka yanzu ana nan ana ta cike-ciken takardu tsakanin Gwamnatin Saudiyya da iyalan mamacin,” in ji Ministan.
Mohammed Idris ya ce idan an kammala za a ɗauko gawar daga Hadaɗɗiyar Daular Larabawa zuwa Saudiyya.
Ya ƙara da cewa tuni ofishin jakadancin Nijeriya a Saudiyya da iyalan mamacin suka kammala shirye-shiryen jana’izar.
Alhaji Aminu Ɗantata yana da burin binne shi a birnin Madina, inda kuma ’yan uwansa suka nemi amincewar hukumomin Saudiyya game da buƙatar kuma aka sahale musu.
Tun da safiyar Litinin ce tawagogin Gwamnatin Tarayya da na Gwamnatin Kano suka tafi Saudiyyar domin halartar jana’izar da aka shiryi yi a ranar Litinin din.
Daga cikin tawagogin akwai Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da Gwamnan Jigawa, Umar Namadi da kuma Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II.
Haka kuma, akwai tawagar Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Ministan Tsaro, Muhammad Badaru Abubakar da kuma malamai irinsu Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa da Dakta Bashir Aliyu.
Aminiya ta ruwaito cewa a ranar Asabar da ta gabata ce dai bajimin ɗan kasuwa Aminu Ɗantata ya rasu yana da shekara 94 da haihuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Aminu Ɗantata
এছাড়াও পড়ুন:
HOTUNA: Yadda Sarki da Gwamnonin Kano da Jigawa suka sauka a Madina domin jana’izar Dantata
Tawagar Sarki Muhammadu Sanui II da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da Gwamnan Jigawa Umar Namadi sun sauka a Madina domin halartar jana’izar Alhaji Aminu Dantata.