Aminiya:
2025-08-16@00:59:28 GMT

Sai bayan Magariba za a yi wa Dantata jana’iza a Madina

Published: 1st, July 2025 GMT

Bayanai daga makusantan fitaccen attajirin nan da ya riga mu gidan gaskiya, Alhaji Aminu Ɗantata sun nuna cewa an ɗage jana’izarsa da aka shirya gudanarwa bayan sallar La’asar a ranar Talata.

Yanzu an mayar da jana’izar zuwa bayan Magariba a haramin birnin Madina.

Kotu za ta duba yiwuwar ba da belin Tukur Mamu a ranar 22 ga watan Yuli Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu

A wata zantawa da ya yi da BBC, Mustapha Junaid, mataimaki na musamman ga marigayin ya bayyana cewa tuni gawar Alhaji Aminu ta isa birnin na Madina.

“Alhamdu lilLah an ɗauki marigayi Alhaji Aminu Ɗantata daga filin jirgi na Madina kuma yanzu haka za a je Shakzura inda a nan ne za a ƙarasa shirya shi kafin daga bisani a kai shi haramin Madina domin gudanar da sallah kamar yadda hukumomin Saudiyya suka amince,” in ji Mustapha Junaid.

Wannan dai shi ne karo na biyu da ake sauya lokacin jana’izar mamacin wanda da farko aka ruwaito cewa za a gudanar a ranar Litinin kamar yadda Ministan Labarai, Mohammed Idris ya tabbatar.

A karon na farko dai, Ministan ya ce an ɗage jana’izar sakamakon rashin isar gawar marigayin a kan lokaci zuwa birnin Madina.

A cewarsa, “akwai ƙa’idoji da Gwamnatin Saudiyya ta shimfiɗa kan yadda za a shigar da gawa domin yi mata jana’iza a ƙasar.

“Saboda haka yanzu ana nan ana ta cike-ciken takardu tsakanin Gwamnatin Saudiyya da iyalan mamacin,” in ji Ministan.

Mohammed Idris ya ce idan an kammala za a ɗauko gawar daga Hadaɗɗiyar Daular Larabawa zuwa Saudiyya.

Ya ƙara da cewa tuni ofishin jakadancin Nijeriya a Saudiyya da iyalan mamacin suka kammala shirye-shiryen jana’izar.

Alhaji Aminu Ɗantata yana da burin binne shi a birnin Madina, inda kuma ’yan uwansa suka nemi amincewar hukumomin Saudiyya game da buƙatar kuma aka sahale musu.

Tun da safiyar Litinin ce tawagogin Gwamnatin Tarayya da na Gwamnatin Kano suka tafi Saudiyyar domin halartar jana’izar da aka shiryi yi a ranar Litinin din.

Daga cikin tawagogin akwai Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da Gwamnan Jigawa, Umar Namadi da kuma Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II.

Haka kuma, akwai tawagar Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Ministan Tsaro, Muhammad Badaru Abubakar da kuma malamai irinsu Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa da Dakta Bashir Aliyu.

Aminiya ta ruwaito cewa a ranar Asabar da ta gabata ce dai bajimin ɗan kasuwa Aminu Ɗantata ya rasu yana da shekara 94 da haihuwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aminu Ɗantata

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Radda ya miƙa wa mataimakinsa ragamar mulkin Katsina

Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda, ya sanar da miƙa wa mataimakinsa, Malam Faruk Jobe, ragamar mulkin jihar, inda shi kuma zai tafi hutun mako uku domin duba lafiyarsa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labaran jihar, Bala Salisu Zango, ya fitar a ranar Alhamis.

Sanarwar ta bayyana cewa hutun zai fara ne daga ranar Litinin, 18 ga watan Agusta, 2025.

An zabi sabuwar firaminista a Luthuania Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC

A cewar Gwamna Radda, hutun zai ba shi damar samun kulawar likitoci da kuma tabbatar da cewa zai ci gaba da gudanar da ayyukansa cikin koshin lafiya.

“Cikin matakan da nake ɗauka don kula da lafiyata da kuma ganin na yi aiki cikin yanayi mai kyau, na ɗauki wannan matakin tafiya hutu, kuma zan dawo da zarar likitoci sun gama duba ni,” in ji gwamnan a cikin sanarwar.

A watan Yuli ne gwamnan ya gamu da hatsarin mota a kan hanyar Katsina zuwa Daura, lamarin da ya jawo damuwa a tsakanin jama’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 Ta Imam Hussain (a) A Bana
  • Duniyarmu A Yau: Ranar 40 na Imam Hussain (a) Na Bana
  • Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
  • Gwamna Radda ya miƙa wa mataimakinsa ragamar mulkin Katsina
  • An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati
  • Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16
  • Ranar Matasa: Ciyaman ya jinjina wa gwamnatin Gombe kan ɗaukar matasa aiki
  • Kungiyar SSANU Ta Ba Gwamnatin Taraba Wa’adin Sati Biyu Akan Kudaden Albashin Da Ba A Biya Ba.
  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura