Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota
Published: 3rd, July 2025 GMT
Magoya bayan Liverpool da masoya ƙwallon ƙafa a faɗin duniya na cikin jimami bayan ɗan wasan Portugal, Diogo Jota, ya rasu a wani hatsarin mota.
Hatsarin ya auku ne da safiyar ranar Alhamis a yankin Zamora na ƙasar Spain.
’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya FuskantaJota ya rasu yana da shekara 28 a duniha.
Hatsarin ya faru ne a hanyar A-52, kusa da garin Palacios de Sanabria.
Jota yana cikin motar tare da ɗan uwansa, André Silva, wanda shi ma ya rasu.
Silva ɗan wasa ne da ke taka leda a ƙungiyar ƙwallon kafa ta Penafiel a ƙasar Portugal.
Rahotanni sun ce motar ta ƙwace ne tare da barin hanya sannan kuma ta kama da wuta.
Jami’an agaji da ma’aikatan kashe gobara daga Rionegro del Puente sun isa wajen cikin gaggawa, amma ba su iya ceto rayuwar mutanen da ke cikin motar ba.
Hukumomi har yanzu suna bincike don gano musabbabin aukuwar hatsarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Wasa hatsarin mota Zamora
এছাড়াও পড়ুন:
An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro
Sufeton ƴansanda na Ƙasa, IGP Kayode Egbetokun, ya maye gurbin Kwamishinan ƴansandan birnin tarayya, CP Ajao Adewale, sakamakon ƙaruwar matsalolin tsaro a Abuja. Wannan mataki ya biyo bayan matsin lamba da yake fuskanta saboda rashin gamsuwa da aikinsa tun bayan karɓar ragama daga CP Benneth Igwe.
Majiyoyi daga cikin rundunar sun bayyana cewa sauya shi ya shafi yadda matsalolin tsaro ke ƙaruwa a Abuja, musamman bayan harin fashi da makami da ya yi sanadin mutuwar mai gabatar da shirye-shiryen gidan talabijin ɗin ARISE, Somtochukwu Maduagwu, da mai gadi Barnabas Danlami, a Katampe, ranar 29 ga Satumba, 2025.
Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A AbujaWata wasiƙar cikin gida daga shalƙwatar ƴansanda ta tabbatar da cewa CP Miller Gajere Dantawaye ne aka naɗa sabon kwamishinan ƴansanda na FCT, yayin da DCP Wilson Aniefiok Akpan aka tura shi zuwa jihar Kogi.
Wasiƙar, mai lamba TH.5361/FS/FHQ/ABJ/SUB.6/213, ta bayyana cewa wannan sauyin na ɗan lokaci ne har sai hukumar aiyukan ƴansanda ta ƙasa (PSC) ta amince da cikakken naɗin.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA