Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta bayyana a yau cewa, a shekarun baya-baya nan, an gwada sabbin kayayyayin fasahohin zamani kamar mutum-mutumin inji mai siffar dan Adam, da gilas na zamani, da na’urorin ba da jinya dake hade da kwakwalwa da inji da sauransu, a dandalin bikin baje koli na kayayyakin shige da fice na Guangzhou wato Canton Fair, da bikin baje koli na kayayyakin sayayya na kasa da kasa, da bikin baje koli na kayayyakin da ake samarwa na kasa da kasa wato CISCE da sauransu.

Wadannan bukukuwan baje koli sun shaida sabon karfin Sin na samar da hajoji da hidimomi masu karko, kana sun kasance muhimmin gadar dake hade sassan kasa da kasa kan mu’amalar kimiyya da fasahohi, ko hakan ya shaida tunanin kasar Sin na raya fasahohi, da yin kirkire-kirkire mai bude kofa ga kowa, da samun moriyar juna.

Mao Ning ta bayyana cewa, kasar Sin ta gudanar da kirkire-kirkire don raya kanta, har ma da samar da moriya ga dukkanin duniya baki daya. Sin tana kuma fatan yin kokari tare da sauran sassan kasa da kasa wajen sa kaimi ga raya fasahohin zamani, ta hanyar hadin gwiwa da bude kofa, da ci gaba da zamanintar da kasashen duniya, ta hanyar yin kirkire-kirkire. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

 Iran: Babu Wani Alfanu A Ci Gaba Da Bai Wa IAEA Hadin Kai

 Kwamitin koli na  tsaron kasa a cikin majalisar shawawar musulunci ta Iran ya bayyana cewa; Saboda yadda hukumar makamashin Nukiliya ta kasa da kasa ( IAEA) take ci gaba da siyasarta na nuna wariya, ci gaba da aiki da ita ba shi da wani alfanu a wurin Iran.

 Shugaban kwamitin tsaron kasar a majalisar shawarar musulunci ta Iran Ibrahim Azizi ya bayyana cewa; Karkataccen rahoton da hukumar makamashin Nukiliyar ta kasa da kasa ya gabatar ne ya zama abinda HKI ta fake da shi wajen kawo wa Iran hari na ta’addanci.

Azizi ya kara da cewa; Iran ta sha nanata cewa, shirinta na Nukiliya na zaman lafiya ne, kuma yana gudana ne a karkashin yarjejeniyar hana yaduwar makaman Nukiliya.

Ibrahim Azizi ya kuma kara da  cewa; A lokuta da dama Iran ta karbi bakuncin shugaban hukumar makamashin Nukiliyar ta kasa da kasa Grossy, ya kuma ziyarci cibiyoyin makamashin Nukiliya; amma wannan hukumar ta daina aiki da ilimi da kwarewa ta koma abin wasa a hannun manyan kasashe.

Haka nan kuma ya ce; Saboda yadda hukumar ta koma aiki da siyasar nuna wa Iran wariya, ci gaba da yin aiki da ita ba shi da wani alfanu ga Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban kasar Iran ya soki lamirin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA
  • Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba
  • Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
  •  Iran: Babu Wani Alfanu A Ci Gaba Da Bai Wa IAEA Hadin Kai
  • Nijeriya ce kasa ta 12 mafi talauci a duniya — IMF
  • Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
  • An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
  • Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi
  • Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya