David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu
Published: 2nd, July 2025 GMT
Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, ya fice daga jam’iyyar adawa ta PDP.
A cikin wata wasiƙar da Aminiya ta gani, David Mark ya bayyana cewa ya fice daga jam’iyyar ne saboda rikice-rikicen shugabanci da aka gaza magancewa.
Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a JosYa ce waɗannan matsalolin sun kawo wa jam’iyyar naƙaso kuma sun jawo mata abun kunya a idon jama’a.
A daren ranar Talata, an naɗa David Mark da tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, a matsayin shugabannin riƙon kwarya (Shugaba da Sakatare) na wata sabuwar jam’iyyar ADC.
Wannan jam’iyya wadda ta haɗa manyan ’yan adawa na da niyyar ƙwace mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.
A wasiƙarsa, Mark ya ce: “Na tsaya tsayin daka a PDP tun daɗewa, har lokacin da wasu suka bar jam’iyyar bayan faɗuwa zaɓen 2015.
“Amma yanzu jam’iyyar ta lalace, ba ta da tasiri ko haɗin kai. Bayan yanke shawara da iyalina da abokan siyasa, na yanke shawarar shiga sabuwar haɗakar siyasa domin ceto dimokuraɗiyya.”
Sabuwar haɗakar siyasar ta ce za ta ƙalubalanci Tinubu a zaɓe mai zuwa domin ƙwace mulki daga hannunsa.
Amma jam’iyyar APC mai mulki ta ce ba ta jin tsoron haɗakar da manyan ’yan adawa ke yi.
Muƙaddashin Shugaban jam’iyyar APC, Ali Bukar Dalori, ya shaida wa BBC cewa babu wanda ke yin magana a kan wannan haɗaka sai a Abuja.
Ya ce: “Ba mu damu da wannan haɗaka ba. APC jam’iyya ce da mutane ke so. Sabuwar haɗaka ba ta da abin da za ta bai wa jama’a.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: David Mark Haɗakaz ADC Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Shugabannin jam’iyyar APC a matakin gunduma na Gayam, cikin ƙaramar hukumar Lafia, sun dakatar da shugaban jam’iyyar a matakin jiha, Hon. Aliyu Bello. Sun zarge shi da aikata abubuwan da suka saɓa da kundin tsarin mulki na jam’iyyar, musamman sashe na 21 (D)(i–iii), wanda ya haɗa da cin amanar jam’iyya da goyon bayan ɗan takarar wata jam’iyya daban.
Shugaban gundumar, Ibrahim Ilyasu, ya bayyana cewa matakin dakatarwar ya fara aiki nan take, kuma Hon. Bello ba zai iya wakiltar kansa ko amfani da matsayin sa a matsayinsa na mamba na APC daga Gayam ba, har sai an warware batutuwan da aka gabatar. Sun kuma zarge shi da jawo wa jam’iyyar tozarci da keta mutuncinta a idon jama’a.
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A KanoSai dai wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyar a jihar sun ce wannan matakin wani yunkuri ne daga wani ɓangare na ƙungiyar siyasa da ke ƙoƙarin kifar da Bello daga kujerarsa, musamman bisa alaƙa da wani ɗan takarar gwamna a jihar. Sun ce wannan rikici ya ƙara bayyana rabuwar kai da rikicin cikin gida a jam’iyyar.
A wata ganawa da wasu shugabannin jam’iyyar a Lafia, an kaɗa ƙuri’ar nuna goyon baya da amincewa da shugabancin Hon. Bello, wanda hakan ke nuna cewa har yanzu akwai sassa a jam’iyyar da ke goyon bayansa, duk da dakatarwar da aka sanar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp