Aminiya:
2025-10-13@18:09:51 GMT

David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu

Published: 2nd, July 2025 GMT

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, ya fice daga jam’iyyar adawa ta PDP.

A cikin wata wasiƙar da Aminiya ta gani, David Mark ya bayyana cewa ya fice daga jam’iyyar ne saboda rikice-rikicen shugabanci da aka gaza magancewa.

Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos

Ya ce waɗannan matsalolin sun kawo wa jam’iyyar naƙaso kuma sun jawo mata abun kunya a idon jama’a.

A daren ranar Talata, an naɗa David Mark da tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, a matsayin shugabannin riƙon kwarya (Shugaba da Sakatare) na wata sabuwar jam’iyyar ADC.

Wannan jam’iyya wadda ta haɗa manyan ’yan adawa na da niyyar ƙwace mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

A wasiƙarsa, Mark ya ce: “Na tsaya tsayin daka a PDP tun daɗewa, har lokacin da wasu suka bar jam’iyyar bayan faɗuwa zaɓen 2015.

“Amma yanzu jam’iyyar ta lalace, ba ta da tasiri ko haɗin kai. Bayan yanke shawara da iyalina da abokan siyasa, na yanke shawarar shiga sabuwar haɗakar siyasa domin ceto dimokuraɗiyya.”

Sabuwar haɗakar siyasar ta ce za ta ƙalubalanci Tinubu a zaɓe mai zuwa domin ƙwace mulki daga hannunsa.

Amma jam’iyyar APC mai mulki ta ce ba ta jin tsoron haɗakar da manyan ’yan adawa ke yi.

Muƙaddashin Shugaban jam’iyyar APC, Ali Bukar Dalori, ya shaida wa BBC cewa babu wanda ke yin magana a kan wannan haɗaka sai a Abuja.

Ya ce: “Ba mu damu da wannan haɗaka ba. APC jam’iyya ce da mutane ke so. Sabuwar haɗaka ba ta da abin da za ta bai wa jama’a.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: David Mark Haɗakaz ADC Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa Maryam Sanda afuwa, wadda aka yanke wa hukuncin kisa a shekarar 2020 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello, ɗan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Alhaji Haliru Bello.

Maryam,’ mai shekara 37, ta shafe shekaru shida da watanni takwas a gidan yarin Suleja kafin yi mata afuwa.

Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro

Rahotanni sun nuna cewar an yi mata afuwar ne bayan yin nadama da aikata kyakkyawan halaye.

Iyayen Maryam sun roƙi gwamnati da ta sake ta saboda ’ya’yanta biyu da ta ke da alhakin kula da su, tare da alƙawarin sauya halayenta.

Shugaba Tinubu, ya kuma yi wa wasu mutane afuwa da suka haɗa da Manjo Janar Mamman Vatsa, Ken Saro-Wiwa, da kuma Sir Herbert Macaulay.

Gaba ɗaya mutane 175 ne shugaban ya yi musu afuwa, ciki har da masu manyan laifuka, tsoffin fursunoni, da waɗanda suka yi kyakkyawan tuba.

Wannan shi ne karon farko da Shugaba Tinubu ya yi amfani da ikon yafe laifi don tausaya wa waɗanda suka aikata laifuka tun bayan hawansa mulki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
  • Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole