Aminiya:
2025-11-27@22:30:22 GMT

David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu

Published: 2nd, July 2025 GMT

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, ya fice daga jam’iyyar adawa ta PDP.

A cikin wata wasiƙar da Aminiya ta gani, David Mark ya bayyana cewa ya fice daga jam’iyyar ne saboda rikice-rikicen shugabanci da aka gaza magancewa.

Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos

Ya ce waɗannan matsalolin sun kawo wa jam’iyyar naƙaso kuma sun jawo mata abun kunya a idon jama’a.

A daren ranar Talata, an naɗa David Mark da tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, a matsayin shugabannin riƙon kwarya (Shugaba da Sakatare) na wata sabuwar jam’iyyar ADC.

Wannan jam’iyya wadda ta haɗa manyan ’yan adawa na da niyyar ƙwace mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

A wasiƙarsa, Mark ya ce: “Na tsaya tsayin daka a PDP tun daɗewa, har lokacin da wasu suka bar jam’iyyar bayan faɗuwa zaɓen 2015.

“Amma yanzu jam’iyyar ta lalace, ba ta da tasiri ko haɗin kai. Bayan yanke shawara da iyalina da abokan siyasa, na yanke shawarar shiga sabuwar haɗakar siyasa domin ceto dimokuraɗiyya.”

Sabuwar haɗakar siyasar ta ce za ta ƙalubalanci Tinubu a zaɓe mai zuwa domin ƙwace mulki daga hannunsa.

Amma jam’iyyar APC mai mulki ta ce ba ta jin tsoron haɗakar da manyan ’yan adawa ke yi.

Muƙaddashin Shugaban jam’iyyar APC, Ali Bukar Dalori, ya shaida wa BBC cewa babu wanda ke yin magana a kan wannan haɗaka sai a Abuja.

Ya ce: “Ba mu damu da wannan haɗaka ba. APC jam’iyya ce da mutane ke so. Sabuwar haɗaka ba ta da abin da za ta bai wa jama’a.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: David Mark Haɗakaz ADC Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu

Shugaba Bola Tinubu ya aike da sunan mutum uku zuwa Majalisar Dattawa, domin tantance su a matsayin sabbin jakadan Najeriya.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne, ya sanar da haka a zaman majalisar na ranar Laraba.

Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna

Waɗanda aka zaɓa su haɗa da Kayode Are daga Jihar Ogun, Aminu Dalhatu daga Jihar Jigawa da kuma Ayodele Oke.

Bayan karanta takardar Tinubu, Akpabio ya ce, “Sunaye uku ne zuwa yanzu, tabbas sauran za su biyo baya.”

Tun bayan ɗarewarsa kan mulki a 2023, Tinubu bai naɗa jakadu ba har yanzu.

Mutane da dama sun daɗe suna ƙorafin kan jinkirin naɗa jakadun.

Amma wasu na ganin aike sunayen jakadun na da alaƙa da barazanar da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na ɗaukar matakin soji a kan Najeriya, kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

A wata hira da aka yi da shi a watan Satumba, Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar, ya ce babu wata matsala game da jinkirin.

Ya ce, “Dukkanin ofisoshin jakadancinmu suna aiki yadda ya kamata. Kowace ofishi yana gudanar da ayyukansa yadda ya dace. Rashin jakadu ba zai haifar da giɓi ba.”

Ya ƙara da cewa duk da cewa jakada shi ne shugaban ofishin jakadanci, akwai kwamishinoni, wakilai da ma’aikatan diflomasiyya da ke tafiyar da harkokin yau da kullum.

A cewarsa, “Diflomasiyya ba aikin mutum ɗaya ba ne. Tsarin ya tanadi irin wannan yanayi.”

Tuggar, ya kuma ce shugaban ƙasa ne kaɗai ke da ikon naɗa jakadu, kuma zai yi hakan a lokacin da ya dace.

Ya bayyana cewa, “Shugaban ƙasa yana duba batun, kuma za a sanar da sunayen a lokacin da ya dace.”

Ya ƙara da cewa, “’Yan Najeriya a ƙasashen waje har yanzu suna samun ayyuka, kuma mu’amala da ƙasashen da muke hulɗa da su ba ta ragu ba.”

Ya ce kuma akwai ƙasashe da dama da suka shafe dogon lokaci ba tare da jakadu ba, amma hakan bai lalata dangantakarsu da wasu ƙasashe ba.

Ya ce, “Wannan ba sabon abu ba ne. Diflomasiyya tana da tanadin irin wannan yanayi. Abin da ya fi muhimmanci shi ne aiki, ba kwaikwayo ba.”

A ƙarshe ya ce Najeriya tana aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran ƙasashen duniya.

“Manufofin ƙasashen waje na Najeriya sun bayyana, kuma ana jinmu a duniya. Abin da muke yi shi ne tabbatar da cewa ofisoshinmu suna samar da sakamako mai amfani ga ’yan Najeriya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Rufai ya koma jami’yyar haɗaka ta ADC
  • ECOWAS ta yi Allah wadai da juyin mulki a Guinea Bissau
  • An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • Sojojin Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar  Guinea Bissau
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
  • Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta
  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia