Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara
Published: 29th, June 2025 GMT
Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya ce zai iya yin komai muddin hakan zai kawo zaman lafiya da ci gaba a jiharsa.
Fubara, ya faɗi haka ne a garin Fatakwal a ranar Asabar, yayin da yake magana da magoya bayansa.
An samu amincewar yi wa Dantata jana’iza a Madina Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester CityYa tabbatar musu cewa ya sasanta da Tsohon Gwamnan jihar, wanda a yanzu Ministan Abuja ne, Nyesom Wike.
Ya ce ya san wasu daga cikin magoya bayansa ba za su ji daɗin sasancin da aka yi ba, amma ya roƙe su da su yi haƙuri.
Ya ce: “Wani lokaci sai an ɗauki matakai masu wahala domin a samu gyara.”
Ya ƙara da cewa: “Kowa ya san mun yi iya ƙoƙarinmu. Amma yanzu abin da muke buƙata shi ne zaman lafiya.”
Fubara ya ce ba wanda zai iya musanta irin taimakon da Wike ya masa.
“E, mun samu saɓani a wasu abubuwa, amma ba za a iya cewa Wike bai taka rawar gani ba.
“Duk wanda ke sona da gaskiya, ya daina magana, lokaci ne na zaman lafiya.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fubara
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD
Gwamnatin kasar Iran ta kai korafi a gaban hukumar kare hakkin bil’adama ta MDD dangane da yakin da HKI da kuma Amurka suka kaiwa kasar na tsawon kwanaki 12, wanda yayi sanadiyyar rasa rayukan mutane fiye da 600.
Nasir Siraj wani jami’in ofishin jakadancin Iran a MDD ya mikawa kwamitionan hukumar Volker Türk a jiya Jumma’a .
Kafin haka dai ministan kiwon lafiya na kasar Iran ya bayyana cewa mutane 627 suka rasa rayukansu a yayinda wasu 4,870 suka ji rauni a yakin kwanaki 12 wanda wadannan kasashe biyu suka keta hurumin sararin samaniyar kasar. Yakin ya zo karshe ne bayan da HKI ta shelanta tsaida yaki ita kadai.
Korafin ya bayyan cewa abinda wadannan kasashe biyu suka yi ya sabawa dokokin kasa da kasa da dama, daga ciki har da dokar kasa da kasa ta kare hakkin bil’adama.