Aminiya:
2025-08-14@03:33:14 GMT

Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara

Published: 29th, June 2025 GMT

Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya ce zai iya yin komai muddin hakan zai kawo zaman lafiya da ci gaba a jiharsa.

Fubara, ya faɗi haka ne a garin Fatakwal a ranar Asabar, yayin da yake magana da magoya bayansa.

An samu amincewar yi wa Dantata jana’iza a Madina Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City

Ya tabbatar musu cewa ya sasanta da Tsohon Gwamnan jihar, wanda a yanzu Ministan Abuja ne, Nyesom Wike.

Ya ce ya san wasu daga cikin magoya bayansa ba za su ji daɗin sasancin da aka yi ba, amma ya roƙe su da su yi haƙuri.

Ya ce: “Wani lokaci sai an ɗauki matakai masu wahala domin a samu gyara.”

Ya ƙara da cewa: “Kowa ya san mun yi iya ƙoƙarinmu. Amma yanzu abin da muke buƙata shi ne zaman lafiya.”

Fubara ya ce ba wanda zai iya musanta irin taimakon da Wike ya masa.

“E, mun samu saɓani a wasu abubuwa, amma ba za a iya cewa Wike bai taka rawar gani ba.

“Duk wanda ke sona da gaskiya, ya daina magana, lokaci ne na zaman lafiya.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Yadda sinadaran dandanon abinci ke yin illa ga lafiya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A yau, yawancin mutane suna amfani da sinadaran dandano wajen girki domin ƙara wa abinci ɗanɗano da ƙamshi. Amma, binciken masana ya nuna cewa ana yawan amfani da su fiye da yadda ake bukata, musamman irin waɗanda aka sarrafa a masana’antu.

Wannan rashin kiyaye ƙa’ida yana iya jawo matsaloli ga lafiya.

Sau da yawa mutane kan manta cewa a cikin waɗannan sinadarai akwai gishiri mai yawa da wasu ƙarin abubuwan da idan aka tara su a jiki na dogon lokaci, suna iya haifar da illa.

NAJERIYA A YAU: Yadda matasa ke bayar da gudunmawa ga ci-gaban al’umma DAGA LARABA: Me Ke Sa Matasa Zama Karnukan Farautar ‘Yan Siyasa A Kafafen Sadarwa Na Zamani?

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne kan irin matsalolin da amfani da sinadarin dafa abinci fiye da kima ke jawowa ga lafiyar mutane.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: A Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe
  • ETFund Ta Koka Kan Gibin Da Ake Samu A Sashin Lafiyar Najeriya
  • DAGA LARABA: Yadda sinadaran dandanon abinci ke yin illa ga lafiya
  • Tinubu Ya Jinjinawa NAFDAC Bisa Matsayin Da Ta Taka A Hukumar Lafiya Ta Duniya
  • Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro
  • An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a Jigawa
  • UNICEF Da Gavi Sun Bada Na’urorin Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Ga Jihar Kano
  • Ya ba wa alaramma kyautar motarsa saboda daɗin karatun Alkur’ani
  • Iran: Babu wani abu da aka yanke game da tattaunawa da Washington