Ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA, ta yi kasafin da dara haka, na wannan adadin, musaman ganin cewa, ta na burin, kara inganta ayyukanta, yadda za su yi dai-dai, da yadda ake gudanar da ayyukan, a sauran Tashoshin Jiragen Ruwa na duniya.

Shugaban Hukumar ya kuma sanar da cewa, a shekarar 2024, Hukumar ta NPA, kudin shigar da ta yi hasashen Tarawa daga na Naira biliyan 865.

39, sun karu zuwa Naira biliyan 894.86.

“ Wannan ya nuna yadda Hukumar ta NPA, ta mayar da hankali da kuma kara zage Damtse wajen ganin ta Tarawa Gwamnatin Tarayya kudaden shiga, masu yawa,”  A cewar Dantsoho.

Shugaban ya kuma bayyana cewa, kudaden shigar da Hukumar ke hasashen Tarawa a shekarar ta 2025, za ta samar da su ne, daga harajin da take karba daga gun Jiregen Ruwan da aka yo jigar kaya wanda ya kai Naira biliyan 544.06 da Naira biliyan  413.06 na Jiragen Ruwa da kuma wasu sauran kudade na Naira biliyan 249.69 sai kuma kudaden shiga, na sasehn gudnar da mulki, da suka kai Naira biliyan  73.07.

Shi kuwa a na sa jawabin, a zaman na Kwamitin, Shugaban Kwamitin Nnolim Nnaji, ya yi kira ga Hukumar ta NPA, da ta kara kaimi kan nasarorin da ta samar, tare da kuma kara inganta kayan da take gudanar da ayyukanta, musaman ta kuma bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kara samar da hanyoyin  ayyukan yi, ga ‘yan kasar nan.

Nnaji ya sanar da cewa, Hukumar ta NPA, ta kasance wata ginshike ce, wajen bayar da gagarumar gudunmawa na kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan.

Shugaban ya kuma bukaci Hukumar da kara mayar da hankali, kan burukan da take son cimma duka manyan kalubalen da take fuskanta.

“Babu kata kasa a fadin duniya da za ta iya samar da wani ci gaba mai dorewa, ba tare da yin aiki, da sanarorin da Hukumar Jiragen Ruwa, ke samarwa ba,” Inji Shugaban.

 

Ya ci gaba da

“Hukumomin Jiragen Ruwa na kowacce kasa a fadin duniya, sune kashin bayan ci gaban tattalin arzikin kasa, musamman kan yadda ake gudanar da hada-hadar fitar da kaya da kuma shigar da su,” A cewar Nnaji.

Kazalika, Shugaban Kwamitin ya sanar da cewa, namijin kokarin da Hukumar ta NPA take kan yi, abin yabawa ne, kuma hakan, zai kara taimaka wa, wajen kara samar da ayyukan yi, a kasar nan.

“Hukumar ta NPA, ba wai kawai tana aikin tara kudaden shiga ba ne, ta kasance wata babbar kadara ce, wajen samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya da kuma kara habaka, tattalin arzikin kasar,” Inji Shugaban.

Nnaji ya bayyana cewa, wannan Kwamtin na jiran ya ga dabarun da Hukumar za ta yi amfani da su, musamman domin kara bunkasa kudaden shigar da kuma kara samar da damar ayyukan yi, ga ‘yan kasar nan, ta hanyar kasafin kudinta, na shekarar  2025.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Hukumar ta NPA Naira biliyan Jiragen Ruwa da kuma kara

এছাড়াও পড়ুন:

An tallafawa iyalan ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta gabatar da cakin kuɗi Naira 13 da dubu ɗari 4 da 28 da ɗari 6 da 59.95 ga ’yan uwan ​​’yan sanda 10 da suka mutu a bakin aiki.

Taron gabatar da kuɗin wanda aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Maiduguri, na da nufin bayar da tallafin kuɗi ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu.

Yadda aka kama mai garkuwa da mutane yana tsaka da cin kasuwar shanu a Neja ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana hakan ne manema labarai a hedikwatar rundunar da ke garin Maiduguri.

Kwamishinan ’yan sanda, CP Naziru Abdulmajid ne ya gabatar da jawabin a madadin Sufeto-Janar na ’yan sanda (IGP), Kayode Adeolu Egbetokun.

Wannan shiri yana ƙarƙashin Ƙungiyar ’yan sandan Najeriya (Group Assurance Life and IGP Welfare Scheme) wanda aka tsara don rage wahalhalun da iyalan ma’aikatan da suka yi sadaukarwa ke fuskanta.

Kwamishina Abdulmajid ya jajantawa iyalan waɗanda suka rasu, yana mai tabbatar musu da jajircewar sufeto-janar na ’yan sanda na tabbatar da jin daɗin jami’an da ke aiki da kuma jaruman da suka mutu.

Ya jaddada cewa, sadaukarwar da waɗannan jami’an suka yi ba za a taɓa mantawa da su ba, kuma rundunar ta ci gaba cewa za ta ci gaba sadaukar da kai wajen tabbatar da jin daɗin iyalan da suka bari.”

Kwamishinan ’yan sandan ya kuma shawarci waɗanda suka ci gajiyar kuɗaɗen da su yi amfani da kuɗaɗen cikin adalci, inda ya buƙace su da su saka hannun jari a harkar kasuwanci mai ɗorewa da zai taimaka wajen tabbatar da makomar waɗanda suka mutu na jami’an na su.

Da yake jawabi a madadin waɗanda suka ci gajiyar shirin, Jerry Joel ya bayyana matuƙar godiya ga rundunar ’yan sandan Najeriya da babban sufeton ’yan sandan ƙasar bisa goyon bayan da suka bayar a wannan lokaci mai cike da ƙalubale a gare su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
  • Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar
  • Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025
  • Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
  • Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador
  • Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
  • An tallafawa iyalan ‘yan sanda da Naira miliyan N13.4m a Borno