Ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA, ta yi kasafin da dara haka, na wannan adadin, musaman ganin cewa, ta na burin, kara inganta ayyukanta, yadda za su yi dai-dai, da yadda ake gudanar da ayyukan, a sauran Tashoshin Jiragen Ruwa na duniya.

Shugaban Hukumar ya kuma sanar da cewa, a shekarar 2024, Hukumar ta NPA, kudin shigar da ta yi hasashen Tarawa daga na Naira biliyan 865.

39, sun karu zuwa Naira biliyan 894.86.

“ Wannan ya nuna yadda Hukumar ta NPA, ta mayar da hankali da kuma kara zage Damtse wajen ganin ta Tarawa Gwamnatin Tarayya kudaden shiga, masu yawa,”  A cewar Dantsoho.

Shugaban ya kuma bayyana cewa, kudaden shigar da Hukumar ke hasashen Tarawa a shekarar ta 2025, za ta samar da su ne, daga harajin da take karba daga gun Jiregen Ruwan da aka yo jigar kaya wanda ya kai Naira biliyan 544.06 da Naira biliyan  413.06 na Jiragen Ruwa da kuma wasu sauran kudade na Naira biliyan 249.69 sai kuma kudaden shiga, na sasehn gudnar da mulki, da suka kai Naira biliyan  73.07.

Shi kuwa a na sa jawabin, a zaman na Kwamitin, Shugaban Kwamitin Nnolim Nnaji, ya yi kira ga Hukumar ta NPA, da ta kara kaimi kan nasarorin da ta samar, tare da kuma kara inganta kayan da take gudanar da ayyukanta, musaman ta kuma bayar da gagarumar gudunmawa, wajen kara samar da hanyoyin  ayyukan yi, ga ‘yan kasar nan.

Nnaji ya sanar da cewa, Hukumar ta NPA, ta kasance wata ginshike ce, wajen bayar da gagarumar gudunmawa na kara bunkasa tattalin arzikin kasar nan.

Shugaban ya kuma bukaci Hukumar da kara mayar da hankali, kan burukan da take son cimma duka manyan kalubalen da take fuskanta.

“Babu kata kasa a fadin duniya da za ta iya samar da wani ci gaba mai dorewa, ba tare da yin aiki, da sanarorin da Hukumar Jiragen Ruwa, ke samarwa ba,” Inji Shugaban.

 

Ya ci gaba da

“Hukumomin Jiragen Ruwa na kowacce kasa a fadin duniya, sune kashin bayan ci gaban tattalin arzikin kasa, musamman kan yadda ake gudanar da hada-hadar fitar da kaya da kuma shigar da su,” A cewar Nnaji.

Kazalika, Shugaban Kwamitin ya sanar da cewa, namijin kokarin da Hukumar ta NPA take kan yi, abin yabawa ne, kuma hakan, zai kara taimaka wa, wajen kara samar da ayyukan yi, a kasar nan.

“Hukumar ta NPA, ba wai kawai tana aikin tara kudaden shiga ba ne, ta kasance wata babbar kadara ce, wajen samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya da kuma kara habaka, tattalin arzikin kasar,” Inji Shugaban.

Nnaji ya bayyana cewa, wannan Kwamtin na jiran ya ga dabarun da Hukumar za ta yi amfani da su, musamman domin kara bunkasa kudaden shigar da kuma kara samar da damar ayyukan yi, ga ‘yan kasar nan, ta hanyar kasafin kudinta, na shekarar  2025.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Hukumar ta NPA Naira biliyan Jiragen Ruwa da kuma kara

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.

Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta tabbatar wa al’ummar jihar a shirye ta ke ta ci gaba da kare mutuncin daidaikun mutane da kungiyoyin da suka sadaukar da kansu domin samar musu da sahihin bayanan sirri da za su kara kaimi wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Nijar.

‘Yan sanda a jihar Neja da ma Nijeriya ƙwararru ne don haka za su ci gaba da aiki da kuma nuna basira da ƙwarewa tare da ƙa’idarta ta sirrin rashin bayyana tushen bayanansu don samun sakamako mafi girma.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja Adamu Abdullahi Elleman wanda ya bayar da wannan tabbacin a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Minna, ya bayyana cewa a kwanan baya ya halarci wani taron bita da hedkwatar ‘yan sanda ta shirya kan masu bada bayanai wato Informant domin kara kwarewarsa.

Sai dai Adamu Abdullahi Elleman ya danganta raguwar ayyukan aikata laifuka a Minna babban birnin jihar da sahihan bayanai da aka samu daga jama’a, goyon baya daga babban sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun da gwamnatin jihar Neja a karkashin jagorancin Gwamna Umar Bago, da sarakunan gargajiya da kuma matakin da ya dauka na cewa a mafi yawan lokuta yakan shiga sintiri a Minna, wanda DPO da kwamandojin yankin suka goyi bayansa.

A cewarsa sakamakon wannan yunkurin da aka yi da dama daga cikin miyagu da suka tsunduma cikin ayyukan ‘yan daba, an kama su, an kuma gurfanar da su a gaban kuliya, tare da daure su a matsayin misali ga wasu.

Adamu Abdullahi Elleman ya ci gaba da cewa, ya kuma gargadi Hakimai na yankin da su rika taimaka wa miyagu cewa duk wanda aka kama za a gurfanar da shi a gaban kuliya manta sabo.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Neja, ya kuma yabawa babbar mai shari’a ta jihar, Mai shari’a Halima Ibrahim bisa goyon bayan da ta bayar wajen ganin an samar da shari’a cikin gaggawa, tare da samun hadin kai tsakanin ‘yan sanda da sauran kungiyoyin tsaro baya ga sabon alkawari da jami’an sa da mazaje suke yi na yakar miyagun laifuka da aikata laifuka a duk lungu da sako na jihar.

Adamu Abdullahi Elleman ya kuma kara da cewa a karkashin sa a matsayinsa na sabon kwamishinan ‘yan sanda mai kula da jihar Neja, jin dadin jami’ansa da jami’an rundunarsa shi ne babban abin da ya fi ba da fifiko wajen kara musu kwarin gwiwa wajen gudanar da ayyuka masu inganci.

INT Aliyu Lawal.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana
  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho