An Kashe Kusan Mutane 1500 Kan Sabanin Mazhaba A Kasar Siriya A Wata Guda
Published: 1st, July 2025 GMT
Mummunan kisan kiyashi kan ‘yan darikar Alawiyyan Siriya, kuma wadanda aka yi wa kisan gilla a kasar a watan Maris sun kai mutane 1,479
A cikin binciken da ya yi na baya-bayan nan, kamfanin dillancin labaran reuters ya bayyana cikakkun bayanai na kisan gillar da aka yi tsakanin ranakun 7 zuwa 9 ga watan Maris din wannan shekara ta 2025, inda aka kai wa ‘yan darikar Alawiyya hare-hare a yankin gabar tekun Siriya.
Kamfanin dillancin labaran reuters ya wallafa binciken nasa ne bisa shaidar fiye da iyalai 200 da abin ya shafa, da kuma hirarraki da jami’an tsaro 40 da mayakan da kuma shugabannin yankin.
Yayin da Majalisar Dinkin Duniya ta watsa rahoton mutuwar mutane 111, inda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya tabbatar da cewa adadin ya fi haka. Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Syrian Network for Human Rights ta watsa rahoton cewa, an kashe mutane 1,334, da suka hada da yara 60 da mata 84, kuma dakarun gwamnati ne ke da alhakin mutuwar mutane 889.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Burtaniya Zata Gurfanar Da mutane 60 Saboda Goyon Bayan Falasdinawa
Mutane kimani 60 ne zasu gurfana a gaban kotu a kasar Burtaniya, saboda goyin bayan kungiyar mai goyon bayan Falasdinu, wata :frre Palastine’ wacce kuma gwamnatin ta bayyanata a matsayin kungiyar yar ta’adda.
Labarin ya kara da cewa wannan shi ne zanga zangar da aka fi kama mutane tun lokacinda aka fara zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa a shekara ta 2023.
Masu goyon bayan Falasdinawa 3 wadanda aka kama a cikin watan Julin da ya gabata, an rika na gabatar da su a gaban kotu kuma kuma za’a tuhumesu karkashin doka da “Yan ta’adda na kasar.
Yansanda sun bayyana cewa kotu tana iya yanke hukuncin zaman gidan kaso har na tsawon watanni 6 a kan ko wanne daga cikinsu.
A jiya jumma’a ce majiyar yansada na birnin London na cewa: tunda a wannan karon sun kama mutane da yawa, wato mutum har 60, to suna iya rarrabasu zuwa gungu-gungu don gabatar da su a gaban kotu karshen dokar nan ‘wacce suke kira ayyukan ta’addanci.
Labarin ya kara da cewa Jam;iyyar Labour ce ta bukaci a sanya kungiyar ‘Action for Palastine, a matsayin kungiyar yan ta’adda.
Kungiyar dai ta saba shirya zanga-zanga a karshen ko wani mako inda dubban mutane sukan shiga don yin Alla wadai da HKI kan kissan kiyashin da take aikatawa a Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Qalibof: Dole Ne Musulmi Su Hada kai Don Matsin Lamba Ga HKI August 16, 2025 Aragchi: Yiyuwan Sake Shiga Yaki Da HKI Nan Kusa Yana Da Wuya August 16, 2025 Putin da Trump sun bayyana aniyarsu ta kawo karshen rashin jituwa da warware batun Ukraine August 16, 2025 Takht-Ravanchi: Iran a shirye take ta ci gaba da tattaunawa kan hakkinta na nukiliya August 16, 2025 Sudan: Al-Burhan ya ce babu sulhu tsakaninsu da dakarun RSF August 16, 2025 Mali: An kama wasu Manyan Sojoji da Wani Bafaranshe bisa zargin yunkurin juyin mulki August 16, 2025 Wata Kotu a Canada ta ayyana APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci August 16, 2025 Hizbullah Ta Ce Ba Zata Ajiye Makamanta Ba August 15, 2025 China Tace Bata Goyon Bayan A Sake Dorawa Iran Takunkuman MDD August 15, 2025 An Gano Gawar Wani Sojan HKI Wanda Ya Kashe Kansa Saboda yakin Gaza August 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci