An ji karar jiniyoyin gargadi a wurare da dama a HKI suna tashi bayan sun hango malamai masu linzami wadanda sojojin Yemen suka cilla daga kasar zuwa haramtacciyar kasar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kafafen yana labaran yahudawan na cewa sun yi shirin kakkabo makaman kafin su isa.

Amma basu bada rahoton yawan barnan da makamai suka yi ba bayan shigowarsu haramtacciyar kasar.

Yahudawan sun bayyana cewa an ji karar jiniyar gargadi a yankunan Beersheba, Dimona da kuma garuruwan da suke kewaye da su a safiyar yau Asabar. 

Majiyar sojojin kasar Yemen sun bayyana cewa sun cilla makaman kan haramtacciyar kasar Isra’ila ne saboda ci gaba da kissan kiyashin da take a zirin gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno

Ana fargabar sojoji da dama sun rasu yayin da mayaƙan Boko Haram suka kai hari sansanin soji da ke Ngamdu, a Ƙaramar Hukumar Kaga a Jihar Borno.

Rahotanni sun nuna cewa mayaƙan sun kai wa sojojin hari a sansanin da ke kan hanyar Maiduguri zuwa Damaturu.

Ɗan Majalisa ya nemi ɗaukar mataki kan dorinar ruwa a Gombe Kwastam ta kama buhunan lalatacciyar fulawa 10,000 ana ƙoƙarin shigo da ita Najeriya

Biyo bayan harin, sojoji sun rufe hanyar Ngamdu har zuwa ƙarfe 11:20 na safe, wanda hakan ya sa matafiya suka maƙale na tsawon lokaci.

“Na tashi daga Damaturu da sassafe ina fatan isa Maiduguri kamar ƙarfe 9 na safe, amma da na isa Ngamdu sai muka tarar da hanya a rufe,” in ji wani matafiyi.

“Jami’an tsaro sun ce mu yi haƙuri saboda an samu matsala a hanya. Daga baya mazauna yankin suka ce Boko Haram ne suka kai wa sojoji hari tare da kashe wasu daga cikinsu.”

Wani mazaunin yankin ya ce mayaƙan sun kai wa sojojin hari ba tare da tsammani ba.

“Harin ya ɗauki lokaci mai tsawo kafin ’yan ta’addan su tafi, amma sun kashe sojoji kuma sun ji wa wasu rauni,” in ji shi.

Wata majiyar tsaro ta tabbatar da faruwar harin, amma ta ce ba a rasa rayuka da yawa kamar yadda aka yaɗa ba.

“‘Yan ta’addan sun yi ƙoƙarin yi wa sojojin kwanton ɓauna, amma sojojinmu jarumai sun yi tsayin daka.

“Wasu daga cikinsu sun ji rauni an kuma kai su asibiti, amma an kashe ’yan ta’adda da dama,” in ji majiyar.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, rundunar sojojin Najeriya ba ta fitar da sanarwa kan harin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk
  • Ammar Hakim Ya Gargadi Kasashen Yamma Da su Kiyayi Tsoma Baki A Harkokin Cikin Gidan Kasar.
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  
  • Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno