Wani ɗan Ghana da aka yi ƙoƙarin yaudararsa shi ma ya tsere, ya koma Ghana, inda ya kai rahoto ga hukumomi, abin da ya haifar da haɗin gwiwar ƙasashen biyu don ceton Sammed.

Sakamakonhaɗin gwiwar da ’yansanda suka yi a Abuja, an ceto Sammed.

Adejobi ya ce an ɗauki matakai don kama waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki domin su fuskanci hukunci.

A wani samame daban, ’yansanda sun kama wasu mutane uku da ake zargi da garkuwa da mutane da kuma ta’addanci a Abuja da Jihar Kaduna.

An kama su ne a ranar 29 ga watan Yuni, 2025, bayan samun sahihin bayani da kuma haɗin kai ƙarƙashin jagorancin ACP Victor Godfrey.

An kama su a wurare daban-daban ciki har da Mpape da Wukushi a Abuja da kuma Rijana a Jihar Kaduna.

Kakakin rundunar ’yansandan Abuja, SP Josephine Adeh, ta ce waɗanda aka kama suna daga cikin gungun masu laifi da ke da sansanoni a dazukan Kachia da Rijana, inda suke tsare waɗanda suka sace na tsawon lokaci.

Hakazalika, an danganta su da wasu hare-hare da suka faru a Jere, Kajuru da wasu sassan Abuja.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yansanda Garkuwa Da Mutane Yaudara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara

Aƙalla jami’an tsaro shida ne suka rasu bayan wata arangama da suka yi da ’yan bindiga a yankin Gada Woro a kan hanyar Patigi da ke Ƙaramar Hukumar Edu a Jihar Kwara.

Waɗanda suka rasu sun haɗa da ’yan banga guda biyar da ɗan sanda ɗaya.

‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’ Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato

Wasu sojoji biyu, ’yan sanda biyu sun samu raunin harbin bindiga a fafatawar da ta faru a ranar Litinin.

Waɗanda suka rasu sun haɗa da Mohammed Nma Dsuru daga Kokodo, Yanda daga Lafiagi, da Ndagi Saraka daga Edogi.

Rahotanni sun ce ’yan bindigar da yawansu ya kai ɗaruruwa sun kai wa tawagar jami’an tsaro farmaki a cikin daji, inda aka yi ta musayar wuta.

Wasu daga cikin waɗanda suka jikkata an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilorin (UITH) domin samun kulawa.

Wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta ya nuna yadda aka fafata a dajin.

Wasu mazauna yankin sun ce lamarin ya fara ne a ranar Asabar, lokacin da aka sace wani fitaccen mai sayar da magungunan gona wanda ya dawo daga aikin Hajji.

’Yan bindigar sun shigo da babura, suka shiga gidansa da ke unguwar Taiwo da misalin ƙarfe 1 na dare sannan suka tafi da shi.

A ranar Lahadi, sun sake kai wani hari inda suka sace ɗan kasuwa mai sana’ar POS, Alhaji Yaman da wani mutum mai suna Usman.

’Yan banga sun samu nasarar ceto mutum ɗaya daga cikinsu.

Wasu daga cikin al’ummar yankin na zargin cewa wasu mazauna garin na taimaka wa ’yan bindigar a ɓoye, duba da cewa yawancin waɗanda aka sace matasa ne kuma fitattun ’yan kasuwa a yankin.

An yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin ’yan sandan jihar, Adetoun Ejire Adeyemi, amma ba ta ɗauki waya ko amsa saƙon da aka aike mata ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi
  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba
  • Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar Haɗaka
  • ’Yan sanda sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa a Jigawa
  • An Kashe Kusan Mutane 1500 Kan Sabanin Mazhaba A Kasar Siriya A Wata Guda
  • Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
  • Togo: An Kashe Mutane 7 A Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati