Aminiya:
2025-08-18@03:36:23 GMT

Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro

Published: 3rd, July 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Yobe, ta sanar da rufe kasuwannin garuruwan Katarko, Kukareta da Buni Yadi saboda barazanar matsalar tsaro.

Wannan mataki na ɗaya daga cikin hanyoyin da gwamnatin ke ɗauka domin inganta tsaro a yankunan.

Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara

Sanarwar ta fito ne daga babban mai bai wa gwamna shawara kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Dahiru Abdulsalam (mai ritaya).

Ya bayyana cewa an yanke wannan hukunci ne domin a samu damar gudanar da wasu ayyuka na musamman da suka shafi tsaro a yankunan da abin ya shafa.

Ya ce wannan matakin na ɗan lokaci ne, kuma yana da nufin tabbatar da ci gaba da samun nasara a yaƙi da ‘yan ta’adda a jihar.

“Ko da yake hakan zai kawo ƙalubale ga al’umma, amma wajibi ne domin a cimma babban burin tsaro,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa gwamnatin na aiki tuƙuru don ganin an rage wa mutane raɗaɗin da wannan mataki zai haifar.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ba da haɗin kai da fahimta don a samu nasarar ayyukan tsaro da kuma wanzar da zaman lafiya gaba ɗaya a jihar.

Har ila yau, ya tabbatar wa al’umma cewa da zarar abubuwa sun daidaita, za a sake buɗe kasuwannin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati kasuwanni Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Za A Sabunta Filin Jiragen Sama Na Ilori Zuwa Cibiyar Jigilar Kayayyaki Ta Zamani

Gwamnatin Jihar Kwara ta ce za ta yi haɗin gwiwa da Hukumar Filayen Jiragen Sama ta Ƙasa (FAAN) da sauran masu ruwa da tsaki domin mayar da jihar cibiyar fitar da kayan gona da na kasuwanci.

Kwamishinan Noma da Ci gaban Karkara na jihar, Dakta Afees Abolore, ne ya bayyana haka a wani taron da Hukumar FAAN ta shirya domin sanar da shirin fara jigilar kayayyaki a Filin Jiragen Sama na Ƙasa da Ƙasa na Janar Tunde Idiagbon da ke Ilori.

A cewarsa, wannan shiri na nufin kara inganta matsayin jihar tare da ƙarfafa rawar da take takawa a harkokin kasuwanci na cikin gida da waje.

Ya jaddada cewa aikin ya yi daidai da manufofin wannan gwamnati na buɗe sababbin hanyoyin fitar da kayayyaki, bunƙasa harkokin kasuwanci, da kuma ƙara samun kuɗaɗen shiga ga masu samar da kayayyaki da  ‘yan kasuwa.

Dakta Abolore ya ce jigilar kayayyakin ta jiragen zai sauƙaƙa daukarsu daga gonaki, zuwa masana’antu, da wuraren sana’o’i zuwa kasuwannin cikin gida da na ƙasashen waje, wanda hakan zai  ƙara musu daraja, sarrafawa da a fannoni daban-daban.

Kwamishinan ya bayyana cewa shirin zai rage asara, ya kiyaye ingancin kayayyaki, sannan ya bunƙasa damar kasuwanci a fannin kayayyakin gona, masana’antu, da kayayyakin da aka sarrafa.

Ya nuna cewa saboda cunkoson da ake samu a tashoshin jiragen sama da na ruwa da ke  Legas, garin Ilori na wata dama ta musamman wajen samun fitar da kayayyaki cikin lokaci da inganci, tare da ƙara wa jihar damar gogayya da jihohi da ma kasashen duniya.

Dakta Abolore ya yi kira ga manoma, ƙungiyoyi, masu masana’antu, masu saka jari, ƙungiyoyin sufuri, ‘yan kasuwa, masu sarrafawa, da hukumomin da ke kula da doka da tsari, da su haɗa kai wajen kara inganci, yadda ake shirya kayayyaki daidai da zamani, da amfani da fasaha domin bin ka’idojin kasuwannin ƙasashen waje.

Shi ma Manajan Filin Jirgin Sama na Janar Tunde Idiagbon, Mista Suraju Aderibigbe, ya bayyana cewa za a sabunta tsohon ginin tashar zuwa sabuwar cibiyar jigilar kaya mai amfani da fasahohi na zamani domin tabbatar da tsaro wajen sarrafa nau’ukan kayayyaki daban-daban.

Ya tabbatar da cewa wannan gyara zai ƙara bunƙasa kasuwanci, samar da ayyukan yi, da kuma ci gaban tattalin arziki a fannoni da dama a jihar.

 

Ali Muhammad Rabi’u 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • AMA Foundation Da FGC Kaduna Sun Hada Kai Domin Tallafawa Ilimin Marayu A Jihar Kaduna 
  • Za A Sabunta Filin Jiragen Sama Na Ilori Zuwa Cibiyar Jigilar Kayayyaki Ta Zamani
  • Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
  • An kafa dokar hana zance tsakanin saurayi da budurwa a Kano
  • Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe
  • Matsalar ƙofa ta hana fasinjoji 58 hawa jirgin Abuja zuwa Landan
  • Matsalar tsaro na iya hana mu ci gaba da rijistar masu zabe a Borno – INEC
  • Ma’aikatan Sufurin Jiregen Sama Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Shirin Sayar Da Filayen Jiragen Sama
  • Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Gina Asibitin Dabbobi A Jihar Kwara
  • Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa