Aminiya:
2025-07-03@14:39:31 GMT

Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro

Published: 3rd, July 2025 GMT

Gwamnatin Jihar Yobe, ta sanar da rufe kasuwannin garuruwan Katarko, Kukareta da Buni Yadi saboda barazanar matsalar tsaro.

Wannan mataki na ɗaya daga cikin hanyoyin da gwamnatin ke ɗauka domin inganta tsaro a yankunan.

Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara

Sanarwar ta fito ne daga babban mai bai wa gwamna shawara kan harkokin tsaro, Birgediya Janar Dahiru Abdulsalam (mai ritaya).

Ya bayyana cewa an yanke wannan hukunci ne domin a samu damar gudanar da wasu ayyuka na musamman da suka shafi tsaro a yankunan da abin ya shafa.

Ya ce wannan matakin na ɗan lokaci ne, kuma yana da nufin tabbatar da ci gaba da samun nasara a yaƙi da ‘yan ta’adda a jihar.

“Ko da yake hakan zai kawo ƙalubale ga al’umma, amma wajibi ne domin a cimma babban burin tsaro,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa gwamnatin na aiki tuƙuru don ganin an rage wa mutane raɗaɗin da wannan mataki zai haifar.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ba da haɗin kai da fahimta don a samu nasarar ayyukan tsaro da kuma wanzar da zaman lafiya gaba ɗaya a jihar.

Har ila yau, ya tabbatar wa al’umma cewa da zarar abubuwa sun daidaita, za a sake buɗe kasuwannin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati kasuwanni Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Uwargidar Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma

Hakazakika, an zakulo Mata dalibai daga wasu zababbun makarantun sakandare a jihar da kuma wasu daidaikun Mata a kananan hukumomi 23 na jihar Kaduna.

 

Da yake kaddamar da Rabon Kayan, Shugaban Ma’aikatar Fadar Gwamnatin jihar Kaduna Malam Liman Sani Kila, ya bayyana gamsuwarsa dangane da kokarin uwargidar shugaban kasa Remi Tinubu na tallafawa Mata Da Matasa a fadin kasar baki daya.

 

Hakazakika, ya jinjinawa Uwargidar Gwamnan jihar Kaduna Hajiya Hafsat Uba Sani bisa bubbasar da takeyi wajen tallafawa Mata Da dalibai Mata Da masa abin a Yaba ne Yana Mai bayar da tabbacin cewa gwamnatin jihar Kaduna Ta himmatu wajen ciyar da aikin Noma a jihar Kaduna.

 

Kila ya kuma jinjinawa Hajiya Hafsat Uba wajen jajircewata wajen Tabbatar da cewa duk wani tallafi na uwargidar shugaban kasa take aikowa Kaduna Yana kaiwa ga mata.

 

Yace Gwamnatin Uba Sani ta ware Kashi 70 cikin dari na kasafin kudin jihar wajen harkar bunkasa aikin Noma Wanda a tarihin jihar Kaduna ba’a taba samun Gwamnatin da tayi irin haka ba.

 

Ya bukaci wadanda suka amfana da tallafin da suyi amfani da Kayan wajen dogoro da kansu maimakon su sayar dasu.

 

Shugaban yace Babu shakka wannan Shirin zai taimakawa ci gaban rkyuwar Mata. Yace Rabon Kayan na wannan karon ba Mata zalla kadai bane Zasu amfana yarda dalibai maza da mata a fadin jihar Kaduna baki daya.

 

Da take nata jawabin uwargidar Gwamnan jihar Kaduna Hajiya Hafsat Uba Sani ta bayyana cewa uwargidar shugaban kasa Remi Tinubu tana da burin tallafawa ci rkyuwar Mata da Yara domin farfado da tattalin arzikin jihar Kaduna Ta bangarori da dama.

 

Tace wannan Shirin zai tamaka wajen bunkasa ci gaban rkyuwar Mata da Yara a fadin jihar Kaduna tana Mai cewa ya zama wajibi daukacin matan jihar Kaduna su nuna goyon bayansu da uwargidar shugaban kasa a kokarin da take da inganta rayuwarsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
  • Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato
  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu
  • Kayan Aro Baya Rufe Katara
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Ba Za A Iya Kawar Da Fasahar Nukiliya Da Karfi Ba
  • Uwargidar Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma
  • Sai bayan Magariba za a yi wa Dantata jana’iza a Madina
  • Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu