Yau Talata ita ce ranar cika shekaru 104 da kafuwar jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin wato JKS. A cikin lokacin sanyi na shekarar 2012, jama’ar kasar Sin sun wayi gari da ganin motocin gwamnati kalilan ne ke kai-komo a kan tituna, kuma an daina amfani da kudin gwamnati wajen shirya liyafar cin abinci a gidajen cin abinci masu tsada, kana hatta kyautar da ake bayarwa ta kek, watau “Mooncake” lokacin bikin tsakiyar kaka an rage girmanta daga dan karamin akwati zuwa wani karamin kunshi.

Wannan shi ne sauyin da aka samu bayan aiwatar da shahararrun “Ka’idoji Takwas” na jam’iyyar JKS. Matakin da aka dauka na dokoki ya zama tamkar wani magani mai karfi wanda ke warkad da “cututtukan” da suka zama matsaloli kamar “sharholiya da kudin gwamnati” wadanda ake ganin ba su taka-kara-sun karya ba amma kuma sannu a hankali suna zubar da kima da martabar jam’iyya mai mulki ta JKS.

Shekaru 13 bayan haka, a lokacin da aka koyar tare da ilmantar da rassan jam’iyyar a dukkan matakai na kasar Sin game da “Ka’idoji Takwas”, wadannan ka’idojin, wadanda tun farko sun mayar da hankali ne kan “magance cin hanci da rashawa tun daga tushe”. Sun tashi daga zama tsarin gina salon gudanar da aiki zuwa gawurtaccen tsarin tafiyar da shugabanci na jam’iyyar.

A karkashin wannan, babban sirrin JKS wajen samun bunkasa da kuma kiyaye nasarar da ta samu a cikin shekaru fiye da dari a tarihi, shi ne juyin juya halin da take yi wa kanta. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido A Karamar Hukumar Gwiwa

Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa Alhaji Aminu Zakari, yace ziyarar kwamatin a kananan hukumomin jihar 27 tana bada damar ganawa kai tsaye a tsakanin masu ruwa da tsaki domin karfafa dabi’ar aiki tare da juna da kuma kyautata alaka a tsakanin bangarori daban daban.

Ya yi wannan tsokaci ne lokacin da ya jagoranci ‘yan kwamatin domin ziyarar aiki a sakatariyar karamar hukumar Gwiwa.

Yace a lokacin irin wannan ziyarar, kwamatin yana duba kundin bayanan sha’anin mulki da na harkokin kudi domin tabbatar da gudanar harkokin kananan hukumomi kamar yadda ya kamata, ta hanyar aiki da tanade-tanade da kuma ka’idojin kashe kudade.

Alhaji Aminu Zakari ya kuma lura cewar Kwamatin yana kafa kananan kwamitoci domin ziyarar gani da ido dan tantance ayyukan raya kasa a lungu da sakon karamar hukumar domin tabbatar da cin moriyar kashe kudaden gwamnati ta hanyar ayyuka masu inganci.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Gwiwa, Malam Muhammad Abubakar Zakari, ya bayyana kwarin gwiwar cewa ziyarar kwamatin za ta zaburar da shugabanni wajen kashe kudade ta hanyar da ta dace, tare da wanzar da shugabanci nagari.

Malam Muhammad Zakari ya kuma sha alwashin bada cikakken hadin kai da goyon baya domin samun nasarar ziyarar.

Kazalika, ya bada tabbacin amfani da shawarwarin kwamatin domin ci gaban karamar hukumar sa.

Sauran ‘Yan kwamatin sun hada da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama, Alhaji Sani Sale Zaburan da wakilin Malam Madori Alhaji Hamza Adamu Ibrahim Babayaro da sakataren Kwamatin da mataimakan sa da Oditoci biyu.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APC ta nemi INEC ta soke zaɓen cike gurbin Kano
  • Zaɓen cike gurbi: An samu ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a Zariya
  • APC ta buƙaci a soke zaɓen cike gurbi a Kano
  • Yadda noma ya kankama bayan sulhu da ’yan bindigar Katsina
  • An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido A Karamar Hukumar Gwiwa
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli
  • NAJERIYA A YAU: Halin ƙuncin da ’yan fansho ke ciki a Najeriya
  • Motar tifa ta murƙushe ɗalibai biyu har lahira a Bayelsa
  • Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9