Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta
Published: 1st, July 2025 GMT
Yau Talata ita ce ranar cika shekaru 104 da kafuwar jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin wato JKS. A cikin lokacin sanyi na shekarar 2012, jama’ar kasar Sin sun wayi gari da ganin motocin gwamnati kalilan ne ke kai-komo a kan tituna, kuma an daina amfani da kudin gwamnati wajen shirya liyafar cin abinci a gidajen cin abinci masu tsada, kana hatta kyautar da ake bayarwa ta kek, watau “Mooncake” lokacin bikin tsakiyar kaka an rage girmanta daga dan karamin akwati zuwa wani karamin kunshi.
Wannan shi ne sauyin da aka samu bayan aiwatar da shahararrun “Ka’idoji Takwas” na jam’iyyar JKS. Matakin da aka dauka na dokoki ya zama tamkar wani magani mai karfi wanda ke warkad da “cututtukan” da suka zama matsaloli kamar “sharholiya da kudin gwamnati” wadanda ake ganin ba su taka-kara-sun karya ba amma kuma sannu a hankali suna zubar da kima da martabar jam’iyya mai mulki ta JKS.
Shekaru 13 bayan haka, a lokacin da aka koyar tare da ilmantar da rassan jam’iyyar a dukkan matakai na kasar Sin game da “Ka’idoji Takwas”, wadannan ka’idojin, wadanda tun farko sun mayar da hankali ne kan “magance cin hanci da rashawa tun daga tushe”. Sun tashi daga zama tsarin gina salon gudanar da aiki zuwa gawurtaccen tsarin tafiyar da shugabanci na jam’iyyar.
A karkashin wannan, babban sirrin JKS wajen samun bunkasa da kuma kiyaye nasarar da ta samu a cikin shekaru fiye da dari a tarihi, shi ne juyin juya halin da take yi wa kanta. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Togo: An Kashe Mutane 7 A Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
Masu fafutuka a kasar Togo sun sanar da cewa an kashe mutane 7 a yayin Zanga-zangar nuna kin jinin gwamnati da aka yi a makon da ya shude, suna masu tuhumar jami’an tsaro da yin amfani da karfin da ya wuce haddi.
Kamfanin dillancin labarun “Reuters” wanda ya nakalto ‘yan fafutukar na kasar Togo, suna cewa; Jami’an tsaro sun yi amfani da karfi mai ban tsoro akan masu Zanga-zangar.”
Kungiyoyin fararen hula da na masu kare hakkokin dan’adam 12 ne su ka fitar da sanarwar, su ka kuma kara da cewa; jami’an tsaron kasar sun yi amfani da kulake wajen dukan masu Zanga-zangar, haka nan kuma igiyoyi da suke daure su, kamar kuma yadda su ka sace da lalata dukiyar mutane.
Har ila yau kungiyoyin sun sanar da samun gawawwakin mutane 3 a ranar juma’ar da ta gabata, 2 daga cikinsu na kananan yara ne da aka jefa a cikin wani tafki a gabashin birnin Lome. Sai kuma gawawwaki 2 na wasu ‘yan’uwa a tafkin yankin Icodesio, shi ma a cikin birnin Lome. Sai a ranar Asabar ne aka sami cikon gawawwakin mutane 2 a yankin Niconakiboyi.
Bayanin da ya fito daga gwamnatin kasar a ranar Lahadi shi ne cewa, mutanen da aka samo gawawwakinsu sun nitse ne a cikin ruwa, tare da taya iyalan wadanda su ka rasa rayukan nasu alhinin rashin da su ka yi.
Masu Zanga-zangar dai suna nuna kin amincewa da yin dandazon mukamkan gwamanti a hannun shugana kasar da kuma rashin Shata hanyar kawo karshen abinda suke ganin a matsayin kama-karya.
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty International” ta bayyana abinda yake faruwa da ‘murkushe ‘yan hamayya.