Faransa Tace Za’a Maida Takunkuman Tattalin Arziki Kan Kasar Iran Idan Taki Yarda Da Yarjeniyar da Trump Yake
Published: 29th, June 2025 GMT
Gwamnatin kasar Faransa ta nawa JMI barazana kan cewa idan bata amince da yarjeniyan da Amurka take so ba to za’a sake dawo da takunkuman MDD a kanta.
Kamfanin dillancin labaran tasnim na kasar Iran ya nakalto ministan harkokin wajen kasar Faransa Jean-Noel Barrot yana fadar haka, ya kuma kara da cewa idan Iran ta ki ta rattaba hannu kan yarjeniyar da gwamnatin shugaba Trump yake so kan shirinta na makamashin Nukliya ba, abinda muke buklata kawai shi ne mu aika da wasika kan a dawoda takunkuman tattalin arziki kan kasar Iran, wadanda suka hada da na makamai, kudade, da kuma fasaha wadanda aka dagesu shekaru 10 da suka gabata.
Bayanda Amurka ta fice daga yarjeniyar JCPOA a shekara 2018 kasashen turai Faransa Burtaniya da Jamus suma sun ki su cika alkawulanda suka hau kansu a yarjeniyar donn goyon bayan Amurka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Da Isra’ila Kanta
Iran ta yi kira da a gudanar da bincike mai zaman kansa kuma a hukumance kan zaluncin ‘yan sahayoniyya da Amurka
Mataimakin babban jami’in kula da harkokin kasa da kasa na ma’aikatar shari’a kuma sakataren hukumar kare hakkin bil’adama ta Iran ya yi la’akari da matakin wuce gona da iri na baya-bayan nan da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka yi kan cibiyoyin makamashin nukiliya, da kafofin yada labarai, da cibiyoyin kiwon lafiya na Iran, da kuma wuraren zama, gidajen yari da birane da kauyuka, a matsayin misali karara na keta dokokin kasa da kasa da hakkokin bil’adama.
A cikin wata wasika da ya aike wa kwamishinan kare hakkin bil-Adama na Majalisar Dinkin Duniya Volker Türk Nasser Seraj mataimakin shugaban hukumar shari’a kan harkokin kasa da kasa kuma sakataren hukumar kare hakkin bil’adama ta kasar Iran ya bayyana cewa da gan-gan yahudawan sahayoniyya sun kai hari kan ginin gidan rediyo da talabijin na Iran da makamai masu linzami.
Ya yi nuni da cewa, wannan harin ya ruguza wasu cibiyoyin yada labaran kasar, tare da kawo cikas wajen yada labarai, sannan kuma abin takaici ma ya kai ga shahada da raunata ma’aikatan kafafen yada labarai wadanda su kadai ke da alhakin sanar da jama’a abubuwan da ke faruwa.
A daya bangaren Saraj ya ci gaba da cewa: Hare-haren da ‘yam sahayoniyya suka kai a kwanakin baya kan cibiyoyin kiwon lafiya, ginin kungiyar agaji ta Red Crescent, da motocin daukar marasa lafiya, da kuma yankunan da ke kusa da asibitoci, sun haddasa lalacewar ababen more rayuwa, wanda ya yi sanadin mutuwa da jikkatar fararen hula, tare da sanya tsoro da firgici a tsakanin jama’a.