Aminiya:
2025-08-15@21:44:15 GMT

NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata 2 bayan ambaliya

Published: 1st, July 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tun bayan da ambaliyar ruwa ya ci wasu sassan garin Mokwa al’ummar yankin suka faɗa halin neman taimako.

Duk da cewa Gwamnatin Tarayya da wasu ɗaiɗakun mutane sun tallafa wa waɗanda abin ya shafa da kuɗi da ma wasu abubuwa, amma mazauna yankin suna bayyana rashin jin daɗinsu bisa yadda al’amura ke gudana a garin.

Najeriya A Yau: Yadda Za A Kawo Karshen Daukar Doka A Hannu A Najeriya DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan halin da al’ummar Mokwa ke ciki watanni biyu bayan ibtila’in ambaliyar.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Mokwa

এছাড়াও পড়ুন:

Kotun kasar Kanada ta ayyana APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci

Wata kotun tarayya a kasar Kanada ta ayyana manyan jam’iyyun Najeriya na APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci yayin da ta hana wani tsohon dan siyasa, Douglas Egharevba, mafaka a kasar saboda alakarsa da jam’iyyun.

Jaridar Peoples Gazette ta rawaito cewa alkalin kotun, Phuong Ngo, a hukuncin da ta yanke ranar 17 ga watan Yunin 2025, ta hana dan siyasar izinin shiga kasar bayan samun shi da gaza cika sharudan dokar shige da fice ta kasar.

A cewar alkalin, “Dabi’ar wasu ’yan siyasa ’yan PDP, wadanda wasu daga cikinsu ma kusoshi ne a jam’iyyar, da wadanda suka aikata laifukan siyasa ko aka yi da yawunsu, ta yi yawan da ba zai yiwu a ki alakanta shugabancin jam’iyyun da ita ba.”

Ana sa ran dai nan ba da jimawa ba gwamnatin Najeriya za ta fitar da sanarwa kan matsayinta a hukumance, kamar yadda wani babban jami’in gwamnati ya tabbatar mana, yana mai bayyana hukuncin a matsayin abin takaici.

Ita kuwa jam’iyyar PDP, ta bakin mamba a kwamitinta na zartarwa, Timothy Osadolor, ta ce kotun na da ’yancin fadin albarkacin bakinta, amma hukuncin nata ba yak an gaskiya.

“Amma babu wata hujja a cikin ra’ayin nasu da zai sa dukkan abin da suka fada a cikin hukuncin nasu ya zama gaskiya,” in ji Timothy.

Ya ce a maimakon ayyana jam’iyya gaba dayanta a matsayin kungiyar ta’addanci, kamata ya yi kotun ta fadi sunan masu alaka da ta’addancin kai tsaye, musamman a cikin jam’aiyyar APC.

Ya kuma bayyana hukuncin a matsayin na yanke kauna da salon shugabancin gwamnatin Najeriya a karkashin Shugaba Bola Tinubu, inda ya bukaci gwamnatin da kada ta dauki lamarin da wasa.

Sai dai duk kokarinmu na jin ta bakin jam’iyyar APC da gwamnatin tarayya ya ci tura ya zuwa lokacin hada wannan rahoton.

Masu magana da yawun APC na kasa, Felix Morka da Bala Ibrahim ba su amsa kira rubutaccen sakon da wakilinmu ya tura musu ba, yayin da kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, shi ma bai amsa sakon da wakilinmu ya tura masa ba.

To said ai wani jami’in gwamnati ya tabbatar da cewa gwamnatin za ta fitar da sanarwa a kan hukuncin a hukumance da zarar ta tabbatar da sahihancin hukuncin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe
  • Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah
  • Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
  • Kotun kasar Kanada ta ayyana APC da PDP a matsayin kungiyoyin ta’addanci
  • NAJERIYA A YAU: Halin ƙuncin da ’yan fansho ke ciki a Najeriya
  • Ba a ba mu dala 100,000 da gwamnati ta mana alƙawari ba — Super Falcons
  • Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci
  • Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin Najeriya
  • Kullum a Kamaru muke kwana, mu yini a Najeriya – Mazauna ƙauyen Borno
  • ETFund Ta Koka Kan Gibin Da Ake Samu A Sashin Lafiyar Najeriya