NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata 2 bayan ambaliya
Published: 1st, July 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Tun bayan da ambaliyar ruwa ya ci wasu sassan garin Mokwa al’ummar yankin suka faɗa halin neman taimako.
Duk da cewa Gwamnatin Tarayya da wasu ɗaiɗakun mutane sun tallafa wa waɗanda abin ya shafa da kuɗi da ma wasu abubuwa, amma mazauna yankin suna bayyana rashin jin daɗinsu bisa yadda al’amura ke gudana a garin.
Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan halin da al’ummar Mokwa ke ciki watanni biyu bayan ibtila’in ambaliyar.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Mokwa
এছাড়াও পড়ুন:
Rasha A Shirye Take Ta Taimaka Wa Najeriya A Fada Da Ta’addanci
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta sanar da cewa kasar a shirye take ta taimaka wa tarayyar Najeriya a fadan da take yi da ta’addanci.
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Rasha Maria Zakharova ce ta bayyana hakan, sannan kuma ta jinjinawa kokarin da gwamnatin ta Najeriya take yi a wannan fagen na kalubalantar masu wuce gona da iri.
Zakharova ta kuma ce, matsayar Rasha ba ta sauya ba akan yadda take kallon ta’addanci a matsayin barazana ga zaman lafiya na duniya.
Haka nan kuma ta ce, Rasha a shirye take ta bayar da taimako da kuma aiki tare da kungiyoyin kasa da kasa da cibiyoyin MDD da kuma tarayyar Afirka.
Dangane da Najeriya, Zakharova ta kara da cewa; Rasha a shirye take ta ci gaba da bai wa Najeriya taimako, kuma sojoji da jami’an tsaron kasar suna da kwarewa mai yawa da su ka samu a fagen fada da ta’addanci.”
Haka nan kuma ta yi ishara da yadda fararen hula da su ka hada mata da yara suke jin jiki matuka saboda ayyukan ta’addanci.
Kasar Najeriya dai tana fama da matsalolin tsaro daga kungiyoyin ta’addanci da su ka hada Bokoharam, Iswap da kuma barayin daji masu garkuwa da mutane.
A cikin kasa da mako daya an sace daliban makarantun arewacin kasar da dama, da hakan ya tilastawa mahukunta rufe makarantu a jihohi masu yawa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Palasdinawa Sun Karbi Gawawwakin Shahidai 15 Daga ‘Yan Mamaya November 27, 2025 Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon Dake Takawa Makiya Birki November 27, 2025 Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa November 27, 2025 An Zabi Iran A Cikin Majalisar Zartarwa Ta Hukumar Yaki Da Makamai Masu Guba Ta Duniya CWC November 27, 2025 HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin November 27, 2025 Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta November 27, 2025 An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki November 27, 2025 Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan November 27, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza November 26, 2025 Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu. November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci