Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
Published: 3rd, July 2025 GMT
Birgediya Janar Abdulsalam ya roƙi jama’a da su bai wa jami’an tsaro haɗin kai, duk da cewa rufe kasuwannin na iya kawo wata matsala ga rayuwar yau da kullum.
“Gwamnati na ƙoƙarin ganin an rage tasirin da rufe kasuwannin ka iya haifarwa ga al’umma. Muna roƙon ku fahimce mu saboda zaman lafiya da tsaro,” in ji shi.
Ya kuma tabbatar wa mazauna yankunan cewa za a sake buɗe kasuwannin nan ba da jimawa ba, idan aka kammala aikin tsaro da ake gudanarwa.
Kasuwannin da aka rufe suna daga cikin manyan kasuwanni a wannan yanki na Jihar Yobe.
Wani mazaunin Kukareta ya shaida wa wakilinmu cewa ba su san dalilin rufe kasuwannin ba, kawai ji suka yi an ce an bayar da umarni daga sama.
Wani ɗan kasuwa daga Buni Yadi da ya nemi a sakaya sunansa ya ce ya ji an ce an rufe kasuwannin ne saboda wasu ’yan kasuwa na sayar wa Boko Haram kayan abinci.
Ya ce, “Ban san da yawa ba, amma abin da na ji shi ne an bayar da umarni a ranar Litinin, suna cewa masu sayar da abinci a waɗannan kasuwanni suna taimakawa Boko Haram wajen siyan kayan abinci.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Boko Haram gwamnati Yobe Rufe Kasuwanni rufe kasuwannin
এছাড়াও পড়ুন:
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Daya daga cikin manyan nasarorin da Dakta Bello Matawalle ya samu shi ne kaimi da aka yi wurin yaki da ta’addanci, ta hanyar kyautata hadin gwiwa da Sojojin kasa, da Sojojin sama da sauran hukumomin tsaro. An yi rugu-rugu da matattaran ‘yan ta’adda a Arewa Maso Gabas, wanda hakan ya yi sanadiyar raguwar hare-hare. A Arewa Maso Yamma kuwa, gagarumar gudummawa da ma’aikatar tsaro a karkashinsa ta amfani da karfin soja ya yi mummunar illa ga matattarar ‘yan ta’adda wanda hakan ya kyautata fata da al’umma ke da shi cewa an kusan share musu hawaye.
2. Kula da walwalar sojoji da karfafa musu gwiwa
Ganin cewa karfin Sojan Nijeriya ya dogara ne a rundunarta, Dakta Bello Matawalle ya inganta hanyoyin walwalar sojojin ta hanyar biyan su kudin alawus a kan lokaci, kyautata matsuguninsu, da kuma samun ingantaccen kiwon lafiya. Wannan ya kara azama wa sojojin da suke gwabza yaki a fagagen fama.
3. Zamanantar da Dakarun Sojoji
Ganin bukatar gaggawa da ke akwai na zamanantar da sojojin Nigeriya, Matawalle ya samar da waraka ta hanyar samar da sabbin makamai na zamani, da jirage marasa matuki don tattara bayanai da kuma kayan ayyuka da sojoji ke bukata lokacin yaki.
Wadannan kayayyaki sun inganta dabarun da sojoji ke amfani da su ta hanyar raguwar yawan sojojin da ke rasa rayukansu da kuma karuwar nasarori a duk lokacin da aka fita ba-ta-kashi.
4. Raguwar sace-sacen mai da zagon kasa wa tattalin arziki.
Tattalin arzikin Nijeriya ya jima na fama da illar da ake masa sakamakon satan danyen mai a yankin Niger Delta. A karkashin jagorancin Matawalle, an samu karuwar aikace-aikacen da suka hada da hadin gwiwar sojojin ruwa wadanda suka hada da lalata cibiyoyin sace danyen mai wanda hakan ya haifar da aruwar danyen mai da ake fitar da kuma karin kudaden shiga ga kasa.
5. Karfafa mu’amala da hadin gwiwa a yankin Afrika da kasa-da-kasa.
Yawancin matsalolin tsaro ya kan wuce iyakar kasa, saboda haka ne Dakta Matawalle bai yi kasa a gwiwa ba wurin daukar matakan kulla kawance da makwabtan asashe irin su Chadi, da Nijar da Kamaru, da sauran kawayen kasashe irin su Amurka, Birtaniya da Tarayyar Turai wanda ya inganta yanda ake tattara bayanai da kuma musayar bayanan sirri. Hakan ya sa ‘yan ta’adda da masu aikata muggan laifuka ke samun wahalar samun maboya.
6. Karfafa kere-keren kayan yaki a gida
Bisa umurnin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar na tunanin dogaro da kai a fannin tsaro, Dakta Bello Matawalle ya yi kokarin agaza wa Hukumar Samar da Kayan Yaki ta Nijeriya (DICON) domin kara samar da makaman yaki a gida Nijeriya. Wannan mataki ya rage dogaro da kasashen waje da kuma karfafa tattalin arzikin tsaron Nijeriya.
Baya ga bangaren yaki, Bello Matawalle yana cigaba da jaddada muhimmancin aiki da al’umma domin dawo da tsaro. Wannan kiranye da yake yi wurin neman tattaunawa, da sasanci da kuma ayyukan cigaba a yankunan da ake rikici sun taimaka matuka gaya wajen dinke rashin yarda tsakanin jami’an tsaro da kuma fararen hula, wanda hakan zai haifar da zaman lafiya mai dorewa.
Jagorancin Bello Matawalle ya nuna aiki ba kama kafar yaro, sabbin dabaru, da kuma kishin kasa. Nasarorinsa ya nuna irin fahimtarsa a matsalolin tsaron Nijeriya da kuma irin niyyar da gwamnati ke da shi wurin magance su.
Bashir Aliyu dan jarida ne mai nazarin al’amuran da suka shafi siyasa da tsaro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp