Leadership News Hausa:
2025-08-14@15:37:44 GMT

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Published: 30th, June 2025 GMT

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojojin Nijeriya sun kashe wani shugaban ‘yan ta’adda Mai Dada a yankin Maru na jihar Zamfara yayin wani farmaki na musamman.

Babban hafsan Soja Manjo Janar Markus Kangye ya bayyana cewa an kama wasu waɗanda ake zargin suna kai wa ‘yan ta’adda kayayyaki, tare da aika wasu masu basu bayanai a jihohin Borno, Kaduna da Edo.

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17 Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

A Borno, Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda uku tare da ƙwato makamai da harsasai da dama, yayin da aka kama wanda ake zargin jigilar kayayyakin ga ‘yan ta’adda a Monguno.

An kuma ƙwato bindigogi da harsasai a jihohin Kaduna da Filato, yayin da aka kama wasu ƴan fashi a Edo da Bayelsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Army yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato

Wani sabon rikici ya barke a jihar Sokoto inda ‘yan bindiga sun kai hari a wani masallaci a kauyen Marnouna da ke karamar hukumar Wurno, inda suka kashe akalla mutum daya tare da yin awon gaba da wasu da ba a tantance adadinsu ba a lokacin da ake sallar isha.

 

Shugaban jam’iyyar APC reshen jihar Sokoto, Alhaji Isah Sadik Achida, wanda ya fito daga yankin ya tabbatar da faruwar harin inda ya jaddada cewa maharan sun kuma kashe shugaban kungiyar masu sayar da babura na yankin a yayin farmakin.

 

Achida ya ci gaba da cewa, kwana biyu kacal kafin harin masallacin, ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyuka biyu da ke makwabtaka da su, Gidan Taru da Kwargaba, inda suka yi garkuwa da wasu mazauna garin tare da jaddada cewa ‘yan bindigar sun kuma kashe wani dan uwa tare da kama iyalansa baki daya.

 

A cewar shugaban jam’iyyar APC, ‘yan ta’addan na kokarin kafa sansani a yankin domin fadada ayyukansu.

 

Achida ya tabbatar wa mazauna jihar cewa gwamnatin jihar da jami’an tsaro suna bakin kokarinsu domin yakar matsalar.

 

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Sakkwato, ASP Abubakar Rufa’i, ya tabbatar wa gidan rediyon Najeriya faruwar lamarin inda ya ce a yanzu ‘yan fashin na kai hare-hare a lokutan damina domin kai hare-haren ba tare da an gano su ba.

 

NASIR MALALI

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya
  • Sojoji sun kashe babban Kwamandan ISWAP, Amirul Fiya a Borno
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Jama’a A Kauyukan Sakkwato
  • Gwamna Bago Ya Yabawa Tinubu Kan Kama Shugaban Kungiyar Ta’addanci A Neja
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida 
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto
  • Iran: Duk Wani Sabon Hari, Zai Fushin Sojojin Kasar
  • Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara
  • A Mali An Kama Sojoji Fiye da 40 Saboda Zargi da Kokarin Juyin Mulki