Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Published: 30th, June 2025 GMT
Sojojin Nijeriya sun kashe wani shugaban ‘yan ta’adda Mai Dada a yankin Maru na jihar Zamfara yayin wani farmaki na musamman.
Babban hafsan Soja Manjo Janar Markus Kangye ya bayyana cewa an kama wasu waɗanda ake zargin suna kai wa ‘yan ta’adda kayayyaki, tare da aika wasu masu basu bayanai a jihohin Borno, Kaduna da Edo.
A Borno, Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda uku tare da ƙwato makamai da harsasai da dama, yayin da aka kama wanda ake zargin jigilar kayayyakin ga ‘yan ta’adda a Monguno.
An kuma ƙwato bindigogi da harsasai a jihohin Kaduna da Filato, yayin da aka kama wasu ƴan fashi a Edo da Bayelsa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Army yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe sojoji 3 a Kebbi
’Yan bindiga sun kashe sojojin Nigeriya guda uku a wani kwanton ɓauna da suka yi masu a lokacin da suke ƙoƙarin hana yin garkuwa da wasu mutane a ƙauyukan ƙananan hukumomin Sakaba da Danko-Wasagu a Jihar Kebbi.
Sojojin da aka kashe an yi masu sutura a babban barikin sojoji da ke garin Zuru, hedikwatar ƙaramar hukumar Zuru.
Mai Martaba Sarkin Zuru Alhaji Sanusi Mika’ilu Sami, ya halarci janazar domin tausayawa da jinjina wa marigayin kan sadaukarwar da suka yi a wurin kare mutanen ƙasa.
Majiyar da ta shaida wa Aminiya ta ce sojojin sun kai ɗauki ne a lokacin da suka samu labarin ’yan ta’addan sun kai farmaki tare da ƙoƙarin yin garkuwa da mutane don neman kuɗin fansa.
Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina ’Yan Najeriya miliyan 60 na fama da taɓin hankali — LikitaSai dai ana jiran bayani daga rundunar soja ta kasa kan wadannan jami’ai nata da aka kashe a fagen daga a yakin jihar Kebbi.