Aminiya:
2025-08-15@13:02:32 GMT

Jami’an tsaro sun tarwatsa taron kwamitin amintattun PDP

Published: 30th, June 2025 GMT

Jami’an tsaro sun hana mambobin Kwamitin Amintattu na Jam’iyyar Adwa ta PDP gudanar da taron da suka tsara gudanarwa.

A safiyar Litinin din nan ne jami’ai da yawa ne suka kutsa cikin zauren da aka tsara gudanar da taron inda suka bukaci wadanda suka hallara da su watse.

Jami’an tsaro da aka jibge a hedikwatar babbar jam’iyyar adawar sun hana mambobin kwamitin amintattu gudanar da taronsu a hedikwatar jam’iyyar.

Har zuwa lokacin hada da wannan rahoto, wasu daga cikin ’yan kwamitin amintattun na PDP suna tattaunawa a kan halin da ake ciki.

Mun samu rahotannin cewa jami’an sun umurci mambohin su bar ofishin jam’iyar domin ganin ba a gudanar da wani taro a ofishin jam’iyar ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami an Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe wani tsohon malami kuma manomi, Andrew Imuekheme, a Jihar Edo.

Lamarin ya faru ne a ranar Talata a garin Ikabigbo, da ke Masarautar Uzairue, a Ƙaramar Hukumar Etsako ta Yamma.

Allah zai kunyata masu ɗaukar nauyin ta’addanci a Zamfara — Gwamna Dauda Dalilan ƙaruwar mace-mace a hanyoyin Najeriya

Rahotanni sun ce Malam Andrew na kan hanyarsa daga gona lokacin da maharan suka tare shi, tare da ɗauke shi zuwa daji.

Wata mata da ta tsere daga hannun maharan ta koma cikin gari tare da sanar wa mafarauta, waɗanda suka fara bincike nan take.

Tuni jami’an tsaro suka umarci manoma da ke da gonaki a kusa da yankin da su koma gidajensu saboda tsaro.

Daga baya, ’yan sa-kai sun gano babur da takalman mamacin.

Bayan zurfafa bincike cikin dare suka gano gawarsa.

Sarkin garin, Cif Braimah Alegeh, ya yi Allah-wadai da kisan tare da bayyana mutanensa a matsayin masu zaman lafiya.

Ya roƙi gwamnati da jami’an tsaro su kawo musu ɗauki.

Wannan shi ne karo na uku da irin wannan kisan ke faruwa a garin.

Shekaru biyu da suka gabata, an kashe wani malamin Katolika da shugaban mafarauta.

Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Moses Yamu, ya ce zai fitar da sanarwa daga baya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin
  • An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun
  • Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9
  • Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ
  • Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohon malamin makaranta a Edo
  • Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki
  • Gwamna Namadi Ya Yaba Wa Kungiyar NBA Bisa Inganta Manufofi Da Ka’idojin Aikin Lauya
  • ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
  • Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila