Aminiya:
2025-10-13@18:09:50 GMT

Jami’an tsaro sun tarwatsa taron kwamitin amintattun PDP

Published: 30th, June 2025 GMT

Jami’an tsaro sun hana mambobin Kwamitin Amintattu na Jam’iyyar Adwa ta PDP gudanar da taron da suka tsara gudanarwa.

A safiyar Litinin din nan ne jami’ai da yawa ne suka kutsa cikin zauren da aka tsara gudanar da taron inda suka bukaci wadanda suka hallara da su watse.

Jami’an tsaro da aka jibge a hedikwatar babbar jam’iyyar adawar sun hana mambobin kwamitin amintattu gudanar da taronsu a hedikwatar jam’iyyar.

Har zuwa lokacin hada da wannan rahoto, wasu daga cikin ’yan kwamitin amintattun na PDP suna tattaunawa a kan halin da ake ciki.

Mun samu rahotannin cewa jami’an sun umurci mambohin su bar ofishin jam’iyar domin ganin ba a gudanar da wani taro a ofishin jam’iyar ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami an Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara

Aƙalla mutum takwas ’yan Ƙungiyar tsaro ta Civilian JTF ko ’yan ƙato da gora aka sanar an kashe a ƙauyen Dan Loto da ke Ƙaramar hukumar Tsafe a Jihar Zamfara.

Harin dai na zuwa ne makonni biyu kacal bayan da wasu ’yan bindiga suka kai hari a wani masallaci tare da kashe wasu masallata biyar ciki har da wani Limami a ƙaramar hukumar.

’Yan Najeriya miliyan 60 na fama da taɓin hankali — Likita Ɗan Majalisa ya nemi ɗaukar mataki kan dorinar ruwa a Gombe

Dan Loto yana cikin yankin Yandoton Daji, unguwar da ’yan bindigar suka kashe masu ibada biyar a ranar 26 ga Satumba, 2025.

Binciken Daily Trust ya nuna cewa, ’yan bindigar sun yi wa ’yan ƙungiyar ta CJTF kwanton ɓauna ne a lokacin da suke amsa kiran da ‘yan bindigar ke yi na tayar da ƙayar baya ga al’ummar garin Dan Loto.

Usman Yusuf Tsafe ya shaida wa Daily Trust cewa an kashe jami’an CJTF ne a lokacin da suke musayar wuta da ’yan bindigar.

“Akwai yuwuwar ’yan binigar sun samu labarin zuwan jami’an CJTF, don haka suka yi musu kwanton ɓauna.

“’Yan bindigar sun kashe su, suka tsere sai dai sun auka wa jami’an CJTF ne, bayan sun kashe biyar daga cikinsu, sai suka koma daji, ba su kai farmaki ga mazauna garin ba,” in ji shi.

Aliyu Danlami, mazaunin unguwar Yandoton Daji, ya ce sun shiga cikin ruɗani sakamakon harin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba
  • Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Tinubu ya tafi Rome don halartar taro kan sha’anin tsaro
  • An Gudanar Da Taron ‘Farkawar Musulmi’ A Nan Tahren Inda Ka Tattauna Batun Falasdinu
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara