Aminiya:
2025-07-03@11:40:30 GMT

Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato

Published: 3rd, July 2025 GMT

Wasu da ake zargin ’yan ta’addan Lakurawa ne, sun kai hari ƙauyen Kwalajiya da ke Ƙaramar Hukumar Tangaza a Jihar Sakkwato, inda suka kashe mutum 15.

Harin ya faru ne da misalin ƙarfe 2 na ranar Talata, lokacin da mutum ke sallar Azahar.

NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta An sa zare tsakanin ‘yan Kannywood da Alhikima

Rahotanni daga mazauna yankin sun ce harin ramuwar gayya ne bayan da al’ummar ƙauyen suka daƙile wani hari da aka kai musu kwanakin baya, inda suka kashe ’yan ta’addan Lakurawa uku ciki har da wani jagoransu.

A wannan sabon harin, ’yan bindigar sun dawo da yawa inda suka fara harbi kan mai uwa da wabi.

“Muna cikin Masallaci muna sallah suka shigo suka fara harbinmu,” in ji wani mazaunin ƙauyen.

“Sun kashe mazajenmu, sun kuma ƙone kayayyakin abinci da shaguna da gidaje.”

’Yan bindigar sun kuma ƙone gonaki da na’urorin sadarwar ƙauyen, sun lalata turakun layin sadarwa, wanda hakan ya sa ba a iya kiran waya waya ko hanyoyin sadarwa.

Yawancin mazauna ƙauyen sun tsere zuwa garuruwan Gidan Madi da Sakkwato domin neman ɗauki.

“Ina zama yanzu da ’yan uwana a cikin gari,” in ji wata mata.

“Muna roƙon gwamnati ta kawo mana jami’an tsaro, ta kuma dawo mana da layin sadarwa domin mu riƙa bayar da rahoton ayyukan ’yan bindigar.”

Wasu mazauna yankin na zargin cewa harin yana da nasaba da yadda ƙauyen ke bijirewa yawaitar tasirin ƙungiyar.

Wani jagoran al’umma ya taɓa gargaɗin mutane da kada su yadda ’ya’yansu mata su auri ’yan ƙungiyar, wanda hakan ya fusata su.

Wani jami’in Ƙaramar Hukumar ya tabbatar da mutuwar mutum 15 tare da raunata wasu bakwai.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar dai ta ce suna nan suna bincike, amma tuni aka tura jami’an tsaro zuwa yankin domin daƙile karin hari.

Ba wannan ne karon farko da ƙungiyar Lakurawa ke kai hari a yankin ba.

A makon da ya gabata, sun kashe mutum takwas a Sabiyo, kuma sun kai hari ƙauyen Baiji.

Haka kuma sun dasa bam a wani waje da ya kashe aƙalla mutum bakwai a garin Gwabro.

“Wannan ’yan ta’adda suna aiki ba tare da ƙaƙƙautawa ba,” in ji Ghazali Rakah, hadimin Shugaban Ƙaramar Hukumar.

“Sun kusan shiga Sanyinna amma suka janye bayan ganin zuwan sojoji.”

Ƙwarrarren masani kan sha’anin tsaro, Squadron Leader Aminu Bala Sakkwato (mai ritaya), ya buƙaci Gwamnatin Sakkwato da ta horar da matasa domin su taimaka wajen kare ƙauyuka da ke da hatsarin fuskantar hare-haren ’yan ta’adda.

“Rundunar tsaro ta ƙasa na da tarin aiki. Muna buƙatar matasa da aka horas, tare da haɗin gwiwar sojoji domin daƙile barazanar,” in ji shi.

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta ce tana aiki kafaɗa da kafaɗa da rundunar soji da ’yan sanda domin inganta tsaro a yankin Tangaza da kewaye.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan ta adda hari Lakurawa Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Ya samu munanan raunuka a harin da aka kai masa, wanda daga baya ya mutu.

Janar Kangye ya ƙara da cewa Danbokolo ya fi Bello Turji tsabibanci, shi ne ya jagoranci harin watan Disamban 2021 a ƙaramar hukumar Shinkafi ta Jihar Zamfara, inda ya ƙone fasinjoji da ransu a cikin mota.

Hakazalika, ya bayyana cewa Danbokolo na amfani da wata ƙwaya mai suna ‘pentazocine’ domin ci gaba da aikata miyagun laifuka.

Yanzu haka, sojojin Operation FASAN YAMA suna ci gaba da neman Bello Turji wanda ya ɓuya.

Janar Kangye ya tabbatar da cewa rundunar sojin Nijeriya tana da ƙwarin gwiwar samar da zaman lafiya a dukkanin sassan ƙasar nan.

Ya kuma roƙi haɗin kan ‘yan Nijeriya don cimma wannan buri.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • ‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’
  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 10 a Borno
  • Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
  • Hare-haren Isra’ila sun kashe mana mutum 935 a yaƙin kwana 12 — Iran