Indomie , shahararriyar kampanin taliyar indomie a Najeriya, ta sanar da kaddamar da sabon gangamin ta mai taken Ingantaccen Abinci Domin Nasara. Wannan gangamin yana jaddada rawar da abinci mai gina jiki kamar Indomie ke takawa wajen ciyar da

nasarar iyalai da Karin lafiyar su a Arewacin Najeriya.

Shekaru da dama kenan da aka san taliyar Indomie da inganci, daɗi da arha a gidajen ‘yan Najeriya.

Tallan talabijin na Ingantaccen Abinci Domin Nasara ya kapu Akan wannan manufa, inda ya ke nuna Indomie a matsayin abokin tafiya wajen cinma nasarar dukkan iyalai na faɗin ƙasa.

Nasara Ta Hanyar Abinci Mai Gina Jiki

An ƙaddamar da gangamin ne a ranar 6 ga Yuni, 2025, Munaso mu kara jaddada

jajircewar Indomie wajen tallafawa iyaye mata da iyalai ta hanyar samar da abinci mai daɗi, mai sauƙin samuwa, Wanda yake cike da sinadaran gina jiki kuma ke inganta girma, kuzahri da cimma burin rayuwa.

Kunshe a cikin tallar na talabijin akwai labarin Binta. yarinya daga arewacin Najeriya

wacce burinta na zama likita ya samo asali ne ta hanyar soyayyarta da abinci mai gina jiki Wanda mahaifiyarta ke ba ta. Za’a iya kallon faifan tallar a Manhajar YouTube, labarin rayuwar Binta da yake jaddada muhimmanci abinci Mai Gina jiki da goyon bayan Ahali.

Tallar ya bada labarin rayuwar Binta ya kuma maida hankali Akan tasirin abinci Mai kyau wajen tallafawa iyali. Da labarin yayi nisa, mun gano Binta tun daga ƙuruciya zuwa

shigarta makarantar koyon aikin likitanci. Hakan ya nuna yadda abinci mai kyau da

goyon bayan Ahali ke taka muhimmiyar rawa wajen cin nasara. Binta ta girma da cin abinci Mai Gina jiki tun farko wato Taliyar Indomie.

Indomie tun da dadewa tana da yakini cewa ciyarwa ba wai ga kawai jiki ba ne. Muna ciyar da mafarkai da makomar kowanne yaro gaba. Shi ya sa muka ƙirƙiri Indomie AI

Career Generator, wata Manhaja ta musamman da ke taimaka wa yara su hangi manyan burinsu ta hanyar hotuna masu kayatarwa da ƙarfafa gwiwa.

Ta ziyartar https://nasarada.indomie.ng kawai, iyaye za su bi wasu matakai masu sauki domin su samar da hotunan yaransu a matsayin likita, lauya, injiniya, da dai sauransu. Wannan wata hanya ce daga gare mu domin kusanta su da mafarkinsu, sanya nasara ta zama mai yuwa, da kuma nuna wa kowane yaro cewa makomarsu tana da amfani, ana iya hangenta, kuma tana dab dasu.

Dauke Da Muhimman Sinadaran Gina Jiki Taliyar

Indomie na dauke sinadarai masu matuƙar amfani ga jiki, kamar su: calcium, iron, protein, Vitamin B da Vitamin A. Duka suna taimakawa wajen girma, bunƙasa kwakwalwa da kuma lafiya mai ɗorewa. Wannan ya saka Indomie ya zama abinci

daddadar abinci mai sauƙin shiryawa, Wanda ya hada kayayyakin bukata da akeso a kowani kalar abinci.

“Muna alfahari na kaddamar da gangamin ‘Nasara Da Indomie’ wanda ke murnar rawar da abinci mai gina jiki ke takawa wajen gina kyakkyawar Rayuwa anan gaba,” in ji Jamiu Abdulrasheed, jami’in tallace tallace a Manhajar zamani na

Indomie “Wannan girmamawa ce ga sadaukarwar da iyaye mata ke yi wajen ciyar da iyalansu da abinci mai amfani, da kuma nuna yadda Indomie ke haɗa daɗin ɗanɗano da gina jiki domin tallafawa nasara.”

An ƙarfafe masu kallo da su duba wannan labari mai saka kaimi na Ingantaccen Abinci Domin Nasara a shafukan sada zumunta: @IndomieArewa a Manhajar Facebook da

@indomie_arewa a Manhajar Instagram.

Indomie Nigeria zata cigaba da jajircewa wajen samar da hanyoyin abinci masu gina jiki ga iyalai da kuma tallafawa hanyarsu ga cinma nasara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ingantaccen Abinci Domin Nasara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta bayyana sabbin nasarorin da ta samu wajen yaƙi da laifuka a jihar, ta hanyar holen mutum 34 da ta kama da aikata laifuka daban-daban.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Rabi’u Muhammad, ya ce wannan ci gaba ya samu ne saboda sabbin dabarun aiki da kuma bayanan sirri da aka samu daga al’umma da hukumomin tsaro.

Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000

A Anguwar Barnawa da wasu wurare a Kaduna, rundunar Operation Fushin Kada ta kama mutane 13 da ake zargi da aikata fashi da makami da satar wayoyi a otel-otel da gidaje.

An ruwaito sun taɓa kashe ɗan sanda a shekarar 2024, kuma suna samun bayanai daga dilolin miyagun ƙwayoyi a wuraren shaƙatawa. A

An ƙwato bindiga ƙirar gida, gatari da adduna 13, mota, kwamfuta huɗu, wayoyi 13 da talabijin huɗu.

Haka kuma, a Nunbu Bashayi da ke Sanga, an kama mutane bakwai da ake zargi da garkuwa da mutane tare da neman kuɗin fansa.

Dukkanimsu sun amsa laifinsu kuma ana neman ragowar waɗanda suke tsere.

A wani samame daban, ’yan sanda sun kama wasu mutane huɗu da ake zargi da aikata fashi, fyaɗe da damfara.

Sun saba kai hari gidajen mutane, ɗaukar kuɗaɗen mutane, aikata fyaɗe sannan su riƙa ɗaukar bidiyo tsoratar da mutane.

A Zariya kuwa, an kama wasu mutane tara da suka haɗa da maza da mata waɗanda ake zargi da yi wa direban Adaidaita sahu fashi ta hanyar zuba masa magani a abin sha.

Rundunar ta kuma kama wani likitan bogi mai suna Adamu Abubakar Muhammed wanda ya yi wa mutane tiyata ba tare da shaidar karatun likitanci ba.

Ya yi amfani da takardun bogi wajen yin aiki na tsawon wata guda kafin a gano shi.

Kwamishinan, ya ce duk waɗanda aka kama suna hannun rundunar, kuma za a gurfanar da su kotu bayan kammala bincike.

Ya gode wa jami’an tsaro da al’umma kan haɗin kai, inda ya yi da a ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin inganta tsaro a jihar da ƙasa baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • Tashar Talabijin ta Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai
  • Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza