Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Published: 29th, June 2025 GMT
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi kira ga mazauna wani kauyen dake yankin Nyingchi na jihar Xizang mai cin gashin kai, da su rungumi akidar ‘yan uwantakar kabilarsu, da samar da yanayin gudanar da rayuwa mai kyau.
Shugaba Xi ya yi kiran ne cikin wasikar da ya mayar ga mazauna kauyen, wadda a ciki ya bayyana fatansa gare su, bayan da ya ziyarci kauyen cikin watan Yulin shekarar 2021.
Shugaba Xi ya kara da cewa, yana fatan karkashin manufofin JKS, mazauna kauyen za su gina yankunan kan iyakoki, tare da kyautata rayuwar al’ummunsu yadda ya kamata, kana za su zage damtse wajen kare kyakkyawan yanayin tuddan yankin, da raya sunan kauyen ta fuskar yawon bude ido, da bayar da gudummawa ga gina yankin kan iyaka mai wadata da daidaito.
Kauyen dai ya shahara sosai a fannin noman itacen Peach. A shekarun baya-bayan nan, ya cimma sabbin nasarori a fannin bunkasa sha’anin yawon bude ido na kauyuka, da karfafa sassan tattalin arziki, da ingiza ‘yan uwantakar kabila. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?
Har yanzu dai gwamnatin Syriya ba ta komai ba game da barna da hasarar rayuka da makamai da kuma jiragen da ake amfani da su da ta sararin samaniyarta ke haifarwa ba.
Shafin Intanet na kafar Enab na kasar Syria ya wallafa wani labari a ranar 15 ga watan Yuni game da shirun da gwamnatin Syriya ta yi kan karakainar da jiragen yaki da makamai masu linzami ke yi a sararin samaniyar kasar.
Wani mai sharhi ya fada wa Enab cewa gwamnatin Syriya ta yanke shawarar tsayawa tsakiya kan lamarin ne kasancewar tana daukar Isra’ila da Iran a matsayin abokan gabarta.
Ya ce: “Babu daya daga cikinsu da za ka bayyana shi a matsayin abokin al’ummar Syriya, kuma dukkaninsu sun taka rawa wajen lalata kasar Syriya.”
Iran na daga cikin manyan kasashen da suka taimaka wa tsohon shugaban Syriya Bashar al-Assad, ita kuma Isra’ila ta kaddamar da daruruwan hare-hare ta sama kan Syriya, kuma ta jibge sojojinta a yankunan tudun mun tsira tun cikin watan Disamba bayan tuntsurar da gwamnatin Assad.
Ya ce gwamnatin Syria a yanzu ta shagalta ne da kokarin daidaita lamurra a cikin gida da kuma karfafa dakon dangantakarta da Turkiyya da kuma kasashen yankin Gulf.
Jaridar da ke kare muradun yankin Larabawa ta ‘Middle East Eye’ ta ruwaito cewa shugaban Turkiyya Receb Tayyib Erdogan ne ya shawarci sabon shugaban Syria Ahmed al-Sharaa cewa kada ya tsoma kansa cikin rikicin.
Saba ka’idar sararin samaniya
Kafar yada labarai ta Syria ta buga rahotanni da dama tana cewa Isra’ila da Iran na karya ka’idojin amfani da sararin samaniyarta, inda ta ce jirage marasa matuka da kuma makamai masu linzami da dama sun fada cikin kasar.
Kafar yada labarai ta Syria – SANA – ta ruwaito cewa wani jirgi mara matuki ya fada kan wani gida a birnin Tartus, kuma daga baya an tabbatar da cewa matar ta rasu sanadiyyar raunukan da ta samu.
Haka nan kafar yada labaran ta SANA ta ruwaito cewa wasu jirage marasa matuka sun fada kan gidajen al’umma a birnin Daraa kuma wani makamai mai linzami ya fada gefen Damascus, babban birnin kasar, inda makamin ya bar wani katon rami.
Sai dai shirun da gwamnatin Syria ta yi kan wannan lamari ya ja hankalin kafafen yada labarai a cikin kasar da kuma kasashen Larabawa.
Yawancin jaridun sun ja hankalin al’ummar kasar cewa kada su kusanci wauraren da makaman ke fadawa.
Sai dai wata majiya ta gwamnati ta karyata ikirarin jaridar Al-Watan, wadda ta ce Ahmed al-Sharaa ya amince wa Isra’ila ta yi amfani da sararin samaniyar Syria wajen samun bayanai kan tafiyar makaman da Iran ke harbawa.
Gidan talabijin na Syria TD da ke da mazauni a Turkiyya ya tattauna da wani mai sharhi, wanda ya ce ya kamata Syria ta kai korafin wajen Majalisar Dinkin Duniya, sannan kuma ta yi amfani da kasashe kawayenta wajen hana karya ka’idojin amfani da sararin samaniyarta.
Gidan talabijin dain ya ce yakin na Iran da Isra’ila ya yi cikas ga zirga-zirgar jirage zuwa kasar da kuma datse kai tallafi ga al’ummar kasar masu bukata.
Wata jarida ta yankin Larabawa, Al-Kuds Al-Arabi ta ce akwia damuwa kan cewa yakin zai kara raunana tattalin arzikin Syria wanda ba ya da karfi, inda ta ce darajar kudin kasar ta Syria ya fadi da kashi 10 cikin dari tun bayan fara yakin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp