Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bayyana cewa: Dokar Majalisar Shawarar Musulunci ta kasar ta dakatar da hadin gwiwa da hukumar IAEA dole ne aiki da ita

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran, Ismail Baqa’i ya bayyana a wani taron manema labarai cewa: Dole ne hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya ta yi aiki nesa da batun siyasa, yana mai nuni da cewa: Dokar Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran kan dakatar da hadin gwiwa tsakanin Iran da hukumar ta IAEA, dole ne yin aiki da ita.

Ya ce wannan doka ta tana nuna damuwa da fushin al’ummar Iran ne dangane da hare-haren wuce gona da iri da aka kaiwa cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran da kuma kisan gillar da aka yi wa masana kimiyyar nukiliyar kasar.

A zaman taron manema labaransa na mako-mako kan taron tunawa da juyayin shahadan Imam Husaini (a.s), Baqa’i ya ce: “A gare su makokin Ashura ba wai kawai zaman makoki ne na wani lamari mai raɗaɗi ba, a’a, abin tunawa ne na al’adu da wayewar al’ummar Iran na rayuwa ta mutuntaka.” Wato kiyaye mutuncin dan’adam, da rashin yarda da mulkin kama karya ta kowace fuska.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Darakta Janar Na Hukumar IAEA Ya Ce; Babu Tabbas Iran Na Da Shirin Mallakar Makamin Nukiliya

Darakta Janar na hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA ya bayyana cewa: Ba zai iya tabbatar da cewa Iran na kera makamin nukiliya ba!

A wata hira da tashar talabijin ta Faransa LCI, Darakta Janar na hukumar kula da makamashin nukiliya ta IAEA Rafael Grossi ya bayyana cewa: Ba zai iya tabbatar da cewa Iran tana kera makamin nukiliya ba.

Grossi dai ya fuskanci tambayoyi da kalubale da dama daga mai gabatar da Shirin, kan ko Iran na daf da kera makamin nukiliya? Ya amsa a cikin halin shakku, yana mai cewa a cikin rahoton ya nisanci zargin Iran da kokwarin kera makamin nukiliya domin babu tabbas kan zargin.

Da aka tambaye shi ko Iran na kera makamin nukiliya? Grossi ya amsa da cewa: “Ba zai iya tabbatar da hakan ba, kuma zai zama rashin gaskiya idan aka ce suna shirin kera makamin nukiliya.”

Da yake amsa tambayar da mai gabatar da shirin ya yi danganr da wasu masu kallon Shirin suna kokwanton ingancin harin da aka kai kan Iran: Grossi ya kare hare-haren wuce gona da irin haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka kan cibiyoyin nukiliyar Iran, da ba su kan ka’ida, yana mai cewa akwai yanayi na uku a cikin dabarun kera makamin nukiliya da ake kira “boyayyen shiri” ko “shirin da bai fito fili ba” inda har yanzu Shirin bai kai matakin kera makamin ba, amma ta mallaki dukkan karfin iko da fasahohin da ake bukata, kuma idan lokaci ya yi, za su iya mallaka. Ya kara da cewa Iraniyawa suna da fatawar haramta mallakar makamin nukiliya da sauran makaman kare dangi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kakkausar Suka Kan Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta IAEA
  • Shugaban kasar Iran ya soki lamirin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA
  • Iran Tana Tababa da Ayyukan Hukumar Makamashin Nukl’ila Ta MDD Wato IAEA A  Halin Yanzu
  •  Iran: Babu Wani Alfanu A Ci Gaba Da Bai Wa IAEA Hadin Kai
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Matsayin Kasarsa Na Rashin Mika Wuya Ga ‘Yan Kama Karya
  • Darakta Janar Na Hukumar IAEA Ya Ce; Babu Tabbas Iran Na Da Shirin Mallakar Makamin Nukiliya
  • Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar
  • Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD