Muhsin Rizai: Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Bayar Da Umarni Da Jagorantar Yakin “Wa’adussadiq 3”
Published: 3rd, July 2025 GMT
Tsohon kwamandan dakarun kare juyin musulunci na Iran Muhsin Rizai ya bayyana cewa; Jagoran juyin musulunci Ayatullah sayyid Ali Khamnei ne ya jagoranci da kuma bayar da umarnin yakin “Wa’adussadiq 3” akan HKI.
Dr. Muhsin Rizai wanda ya gabatar da jawabi a wurin taron girmama shahidai da aka yi a jiya Laraba a babban masallacin juma’a na Tehran ya kara da cewa; A karon farko jagoran juyin musulunci ne ya rika bayar da umarni da kuma jagorantar yadda yaki da HKI ya kasance.
Dr. Muhsin Rizai wanda shi ne kwamandan dakarun kare juyin musulunci na Iran a lokacin kallafaffen yaki da Iraki, ya kuma ce; An yi aiki tare a tsakanin babbar shalkwatar soja ta “Khatamul-Anbiya” da kuma babbar cibiyar Dakarun kare juyin musulunci, inda jagoran ne ya rika bayar da umarni a matsayinsa na babban kwamandan dukkanin rundunonin tsaron kasa, akan yadda yakin ya rika tafiya. “
Da yake Magana akan sake kawo wa Iran hari da ‘yan sahayoniya za su yi, Dr.Muhsin Rizai wanda a halin yanzu memba ne a cikin majalisar fayyace maslahar tsarin musulunci ya ce; Idan hakan ta faru, to martanin da Iran za ta mayar zai fi na baya tsananin da zai fi karfin a iya kwatanta shi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yajin Aikin ASUU: Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya, ta gargaɗi Ƙungiyar Malaman Kami’o’i ta Ƙasa (ASUU), cewa za ta aiwatar da dokar “babu aiki, babu albashi” idan malaman suka ci gaba da yajin aikin da ka iya zai kawo cikas ga harkokin karatu.
A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta fitar da yammacin ranar Lahadi, Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, da Ƙaramar Ministan Ilimi, Suwaiba Sa’id Ahmed, sun ce gwamnati tana da niyyar magance ƙorafe-ƙorafen ASUU ta hanyar tattaunawa cikin lumana.
Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja“Gwamnati ta nuna gaskiya, haƙuri da kyakkyawar niyya a tattaunawarta da ƙungiyar,” in ji sanarwar.
Ministocin sun bayyana cewa yawancin buƙatun ASUU, kamar ƙarin kuɗin koyarwa da inganta yanayin aiki an riga an biya musu.
Sauran matsalolin kuma suna ƙarƙashin kulawar kwamitocin gudanarwar jami’o’i, waɗanda gwamnati ta sake kafawa don su kula da batutuwan da suka rage.
Sai dai duk da waɗannan matakan, ASUU ta zaɓi shiga yajin aiki.
Ministocin sun ce wannan mataki bai nuna haɗin kai ko adalci ga ɗalibai da jama’a ba.
Sun ƙara da cewa: “Gwamnati ta yi tsayin daka wajen tabbatar da zaman lafiya da daidaita karatu a jami’o’i.
“Amma sun yi gargaɗi cewa, dokar “babu aiki, babu albashi” tana nan daram a tsarin dokokin ƙwadago na Najeriya, kuma gwamnati za ta yi amfani da ita idan aka katse harkokin karatu.
Gwamnati ta roƙi ASUU da ta sake tunani tare da dawowa teburin sulhu, inda ta ce ƙofarta a buɗe ta ke don tattaunawa da yin sulhu.