Aragchi: Iran Ba zata Taba Daina Tace Makamashin Uranium A Cikin Gida Ba
Published: 2nd, July 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa shirin makamashin nukliya na kasar Iran kuma na zaman lafiya ya zama abin alfakhari ga mutanen kasar da daukaka. Don haka gwamnati mutanen kasar ba zasu taba yarda a barshi ba.
Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da yake hira da tashar talabijin ta CBS news na kasar Amurka dangane da hare-haren da HKI da kuma Amurka suka kaiwa kasar a cikin watan yuni da ya gabata.
A wani bangare a maganars Aragchi ya bayyana cewa baya ganin Iran zata farfado da tattaunawa da kasar Amurka nan kusa.
Ya ce: Idan har zamu sake shiga tattaunawa da Amurka sai mun tabbatar da cewa Amurka ba zata kuma kai mana hare-hare a dai-dai lokacinda muke tattaunawa ba.
Ya kara da cewa, tare da wannan tunanin muna ganin sake zama da Amurka kan teburin tattauna ba nan kusa ba. Daga karshe ya ce: a duk sanda muka ga dama ta samu, bama rufe kofar tattaunawa da kowa .
Da aka tamabaye shi dangane da shirin makamashin Nukliya na kasar bayan bom da aka jefa masu. Ministan ya ce: Ai ba’a kauda shirin nukliya da bom. Ko babu shi kwata-kwata zamu sake gina wani daga farko. Sannan idan sun baci ne muna iya sake gyaransu sai mu ci gaba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: tattaunawa da
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
A cewarta, shirin ya taimaka wajen noman shinkafa da ta kai kimanin tan 99,452, wacce kuma kudinta ya kai kimanin Naira biliyan 13.527 tare kuma da noman rogo da ya kai kimanin tan 87,237, wanda kudinsa ya kai Naira biliyan 3.925, musamman domin a kara samar da wadataccen abinci da kuma kara bunkasa fannin tattalin arzikin jihar.
Sai dai, ta bayyana cewa; har yanzu a jihar ba a samar da wani cikakken tsari a hukumance ba, a kan tsarin na shirin na CAF wanda hakan ke haifar wa da shirin koma baya a jihar.
Ta yi kira ga sauran masu ruwa da tsaki a fannin bunkasa aikin noma, domin samun riba a jihar da su bayar da hadin kai wajen shiga cikin tsarin na CAF, musamman a bangaren noman shinkafa da rogo da sauran amfanin gona.
Kazalika, ta bukaci mahukunta a jihar da su samar da tsari a hukumance, musamman na dogon zango domin ci gaba da samar da wadataccen abinci a fadin jihar baki-daya.
Shi ma a nasa bangaren, jami’in shirin na jihar; Dakta Emmanuel Igbaukum ya bayyana cewa, masu ruwa da tsaki a jihar, sun nuna sha’awarsu ta shiga cikin shirin tare kuma da sanya shi a cikin tsarin jihar na samar da abinci mai gina jiki.
Ya kara da cewa, shirin zai kuma taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin aikin noma na jihar baki-daya.
A nata jawabin, Babbar Sakatariya a ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci, Pharm. Elijah ta bayar da tabbacin cewa; gwamnatin jihar za ta bayar da kason kudi a kan lokaci tare kuma da yin rangwame wajen sayen kayan aikin noma cikin rahusa.
Ta bayyana cewa, gudunmawar shirin na IFAD ya taimaka matuka wajen kara bunkasa fannin tattalin arziki da kuma fannin aikin noma na jihar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA