Iran ta bukaci gudanar da binciken gaggawa na Majalisar Dinkin Duniya kan harin da yahudawan sahayoniyya suka kai gidan kurkukun Evin

A cikin wata wasika da ya aike wa babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya da shugaban kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniyar, jakada kuma zaunannen wakilin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya, Amir Sa’ed Irawani, ya yi kira da a gaggauta gudanar da bincike mai tsanani kan harin da ‘yan sahayoniyya suka kai gidan yarin Evin da ke birnin Tehran.

A cikin wasikar, Irawani ya rubuta cewa: Wannan harin da aka kai a ranar Litinin, 23 ga watan Yunin wannan shekara ta 2025, an nufi wani gidan yarin farar hula da gangan, wanda hakan ya sabawa dokokin kare hakkin dan Adam na kasa da kasa da kuma muhimman ka’idojin Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya.

A yayin da yake yin Allah wadai da harin, jakadan kasar Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya kara da cewa: Bisa la’akari da irin hadari da kuma munin wannan mugun aiki da aka aikata, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bukaci kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya da babban sakataren Majalisar da su yi Allah wadai da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai wa gidan yarin Evin. Ba tare da wata shakka ba, harin yana matsayin babban cin zarafi ga dokokin jin kai na ƙasa da ƙasa da dokokin haƙƙin ɗan adam na duniya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a Majalisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Wani ɗan Fashi da makami ya rasa ransa bayan da yayi yunƙurin yin fashi a unguwar Dorayi Babba, Unguwar Jakada, Kano. Rahotanni sun bayyana cewa ɓarawon, wanda aka gano sunansa Musa Nuhu, ya kutsa cikin wani gida riƙe da makami, wata wuka da nufin yin fashi a wani gida.

Bayan shiga cikin gidan, ɓarawon ya kai hari kan wasu mata biyu tare da jikkata su. Sai dai wani namiji daga cikin iyalan gidan yai taho mu gama da ɓarawon a cikin wata fafatawa mai zafi da ta jawo raunika a tsakaninsu duka biyu.

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

Kakakin rundunar Ƴansanda ta Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa a shafinsa na Facebook. Ya bayyana cewa an yi nasarar daƙile harin ne sakamakon jarumtar da ɗaya daga cikin mazauna gidan ya nuna.

“An sami nasarar daƙile ɓarawon bayan wata fafatawa da wanda ake yunƙurin kai wa hari ya yi. An garzaya da shi asibiti domin samun kulawa, amma daga baya likitoci suka tabbatar da mutuwarsa sakamakon munanan raunukan da ya samu,”

in ji sanarwar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
  •  HKI:Har Yanzu Matatar Man Fetur Ta Haifa Ba Ta Koma Aiki Ba
  •  Iran Ta Jinjina Wa Matsayar Da Pakistan Ta Dauka Akan Harin Da HKI Ta Kawo Wa Iran
  • Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
  • Majaliar Dokokin Kasar Corsica Ta Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu Sannan Ta Ki Amincewa Da HKI
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Yi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Da Isra’ila Kanta
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Jaddada Cewa: Iran Tana Da Hakkin Tace Sinadarin Uranium A Kasarta
  • An Fara Gudanar Da Jana’izar Shahidan Yakin Kwanaki 12 A nan Tehran